Rundunar wanzar da zaman lafiya ta Operation Enduring Peace ta shirya taro na musamman da masu ruwa da tsaki daga kananan hukumomin Jos ta Gabas, Bassa da Jos ta Arewa a jihar Filato, domin tabbatar da zaman lafiya don gudanar da ayyukan noma a daminar bana cikin lafiya da kwanciyar hankali.

Kamandan runduna ta uku kuma kwamandan Operation ENDURING PEACE, Manjo Janar Folusho Oyinlola, ya yi kira da mahalarta taron su sake sabunta alkawarin samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummar kananan hukumomin Jos ta Arewa, Jos ta Gabas, da Bassa.
Da yake jawabi ta bakin babban hafsan hafsoshin rundunar Birgediya Janar Senlong Sule, game da muhimmancin taron na masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Jos, GOC ya jaddada cewa taron ya zama wajibi don samar da hanyoyin zaman lafiya a yayin da ake fara noma.

A wata sanarwa da kakakin rundunar zaman lafiya ta Operation Enduring Peace, Keftin Chinonso Polycarp Oteh, Kwamandan ya yabawa mazauna kananan hukumomin 3 bisa jajircewar da suka yi na tabbatar da zaman lafiya, tare da bayyana raguwar tashe-tashen hankula a ‘yan watannin da suka gabata, yana mai alakanta zaman lafiyar da aka samu wajen ci gaba da tattaunawa da hadin kan al’umma.
Kwamandan ya kuma ja hankalin masu ruwa da tsakin kan a cigaba da taimatawa wajen tabbatar da ci gaba da aka samdadon kare yankunan daga barazanar tsaro da ke kunno kai.
Manjo Janar Oyinlola ya bayyana damuwarsa dangane da sace-sacen mutane, hare-haren da ake kai wa masu hakar ma’adanai, da kera makamai ba bisa ka’ida ba, da kuma yawaitar kwararowar shanu zuwa yankunan manoma, wanda a tarihi ya kai ga lalata gonaki da kuma daukar fansa da rarrabuwar kawuna dake wanzuwa tsakanin al’umma.
Kazalika, Kwamandan ya bayyana cewa a kwanakin baya babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya amince da turo bataliya ta musamman zuwa jihar Filato da nufin hanzarta shawo kan barazanar da ke kunno kai da kuma karfafa kokarin tabbatar da zaman lafiya da ake ci gaba da yi, wanda tuni ya fara rage fargaba da kai hare-hare a yankin.
Da yake jawabi ga sarakuna da shugabannin addinai da na al’umma da suka halarci taron, GOC ya jaddada muhimmancin karfafa hanyoyin magance rikice-rikicen da suka shafi al’umma, inda ya bukaci masu ruwa da tsaki da su wayar da kan matasan su kan abubuwan da za su tunzura su, kamar barnar gonaki ko sanya guba wa shanu tare da karfafa samar da ka’idojin da al’umma za su bi.
Ya kuma yi kira ga kafafen yada labarai da su yi amfani da ka’idojin da aikinsu ya shimfida, yana mai gargadin cewa rahotanni masu ban sha’awa ko wadanda ba a tabbatar da su ba, sau da dama suna haifar da tashin hankali maimakon gina zaman lafiya.
A karshen jawabinsa, Manjo Janar Oyinlola ya tabbatar da cewa hukumomin tsaro na gudanar da aikinsu na zama masu sasantawa don tabbatar da tsarin mulkin kasa da kuma kare duk wani dan kasa mai bin doka da oda ba tare da la’akari da kabila ko addini ba.
Ya kuma tunatar da taron cewa zaman lafiya wata bukata ce ta gama-gari ba tare da nuna goyon baya ga wasu ba, inda ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa Operation ENDURING PEACE za ta ci gaba da gudanar da ayyukan kawar da maboyar masu aikata laifuka, wanda yace hakan ya dogara ne kacokam kan tabbatar gaskiya da hadin kan al’ummomin yankin.
A nasa bangaren shugaban karamar hukumar Jos ta Arewa Barr. John Kyohroh Christopher ya yaba wa OPERATION ENDURING PEACE da suke aiki ba dare ba rana wajen ganin an samu zaman lafiya a karamar hukumar, bayan kashe-kashen da ya auku a Anguwan Rukuba.
Christopher ya bayyana cewa karamar hukumar za ta ci gaba da hada kai da rundunar, domin tabbatar da zaman lafiya a Jos ta Arewa.
Ya kuma yabawa GOC da shugaban hafsan soji da kuma babban hafsan hafsoshin tsaro bisa rabon tallafin taki ga manoman yankin.
Sarakunan yankin da shugabannin al’ummar Musulmi da Kirista, sun yaba da kokarin da sojoji suke yi, inda suka yi alkawarin tabbatar da cewa za’a gudanar da ayyukan noma cikin kwanciyar hankali.


