Hukumar ‘Yan Sanda Sun Shirya Yarjejeniyar Zaman Lafiya Kafin Fitar da ‘Yan Takara a jihar Gombe
Rundunar Yan sanda ta jihar Gombe ta shirya taron yarjejeniyar zaman lafiya da masu neman takara a jihar gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyu.
Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda mai kula da harkokin kudi da gudanarwa, Muhammad Mustapha, ya ce an shirya taron ne domin tabbatar da zaman lafiya da gudanar da sahihin zaben fidda gwani ba tare da wata matsala ba.
Wakilan masu neman takara da suka hada dana Isa Ali Pantami da Zakariya Jiddah sun yabawa wannan shiri, suna masu cewa zai kara hadin kai, kwarin gwiwa da gudanar da zabe lafiya


