Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali
Published: January 5, 2026 at 8:21 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun kai farmaki wajen hakar ma’adanin gwal na Morila a kasar Mali karshen makon da ya wuce, inda suka kona kayayyakin aikin, kuma suka yi garkuwa da ma’aikatan gurin guda bakwai, kamar yadda wani jami’i a ma’aikatar ma’adanai ta kasar ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Litinin.

Wannan harin yana nuni da kara tabarbarewar tsaro a Mali, wadda ita ce kasa ta uku da ta fi samar da gwal a Afirka, da ke yaki da ‘yan ta’adda da ke da alaka da kungiyar Al-Qaida, wadanda kan kai farmaki ga kadarori na tattalin arzikin kasa, da kayan zuba jari a kasashen waje.

Mutane dauke da makamai, sun kai farmaki inda aka hakar ma’adanin, wanda wani kamfanin kasar Amurka, Flagship Gold ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kasuwanci a shekarar da ta gabata, a cewar wani me magana da yawun ma’aikatar hakar ma’adanai ta kasar Mali.

Wani da ke da masaniya a kan abun ya kara da cewa, sun kokkona kayayyakin aiki, sannan suka yi garkuwa da ma’aikata bakwai, amma duk sun sako su washegari da yamma.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda
Next Post: An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.