Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran
Published: March 4, 2026 at 2:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana ci gaba da gwabza yaki, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa kasar Iran hari, inda suka kashe shugaban ta Ayatollah Ali Khameni. Isra’ila na ci gaba da kai hari Tehran, babban birnin Iran da kuma Beirut, babban birnin Lebanon, inda itama Iran ta mai da martani wajen kai hare-hare sansanonin sojin Amurka dake gabas ta tsakiya, ta kuma rufe mashigin ruwa na Hormuz, inda jiragen dakon man fetur ke ratsawa.

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yiwuwar sojin Amurka cewa zasu yiwa jiragen dakon man fetur dafifi don su samu wucewa ta hanyar mashigin ruwa na Hormuz. Ita kuma Iran ta dau alwashin harbo duk wani jirgi da ya wuce ta nan.

Kasuwannin hada-hadar hannun jari sun rikice, yayin da farashin danyen man fetur ya tashi sakamakon yakin.

A jiya Talata ne kuma aka samu sabanin ra’ayi game da dalilin da ya sa Amurka ta kaiwa Iran hari tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da kuma sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio.

Trump ya ce ya umurci Isra’ila da ta kaiwa Iran hari saboda yana da yakinin Iran na da niyyar fara kawo musu hari. A nasa bangaren shi kuma Marco Rubio ya sha banban, inda ya shaidawa manema labarai ranar Litinin cewa Amurka ta kaiwa Iran hari ne saboda fargabar da ake yi na cewa Iran zata mai da martani game da shirin kaiwa Tehran hari da Isra’ila ta yi.

Ya ce mun san Isra’ila zata kai hari, kuma mun san cewa za’a mai da martani ta kai hari kan sojin Amurka, mun san idan bamu far musu ba zasu yi mana barna me yawa.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama
Next Post: Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro
“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
  • Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu Siyasa
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.