Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran
Published: March 4, 2026 at 2:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana ci gaba da gwabza yaki, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa kasar Iran hari, inda suka kashe shugaban ta Ayatollah Ali Khameni. Isra’ila na ci gaba da kai hari Tehran, babban birnin Iran da kuma Beirut, babban birnin Lebanon, inda itama Iran ta mai da martani wajen kai hare-hare sansanonin sojin Amurka dake gabas ta tsakiya, ta kuma rufe mashigin ruwa na Hormuz, inda jiragen dakon man fetur ke ratsawa.

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yiwuwar sojin Amurka cewa zasu yiwa jiragen dakon man fetur dafifi don su samu wucewa ta hanyar mashigin ruwa na Hormuz. Ita kuma Iran ta dau alwashin harbo duk wani jirgi da ya wuce ta nan.

Kasuwannin hada-hadar hannun jari sun rikice, yayin da farashin danyen man fetur ya tashi sakamakon yakin.

A jiya Talata ne kuma aka samu sabanin ra’ayi game da dalilin da ya sa Amurka ta kaiwa Iran hari tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da kuma sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio.

Trump ya ce ya umurci Isra’ila da ta kaiwa Iran hari saboda yana da yakinin Iran na da niyyar fara kawo musu hari. A nasa bangaren shi kuma Marco Rubio ya sha banban, inda ya shaidawa manema labarai ranar Litinin cewa Amurka ta kaiwa Iran hari ne saboda fargabar da ake yi na cewa Iran zata mai da martani game da shirin kaiwa Tehran hari da Isra’ila ta yi.

Ya ce mun san Isra’ila zata kai hari, kuma mun san cewa za’a mai da martani ta kai hari kan sojin Amurka, mun san idan bamu far musu ba zasu yi mana barna me yawa.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama
Next Post: Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
  • Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
  • Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Kafa Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC Afrika
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.