Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
Published: April 29, 2026 at 2:21 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Kano ta sanar da shirye-shiryen auren gata ga mutane dubu 3,000.

Gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf, ta sanar da wani babban shiri na jin ƙai ga al’umma, inda za ta aurar da mutane dubu 3,000 a lokaci guda, wanda ya ƙunshi maza 1,500 da mata 1,500.

Sanarwar hakan ne ƙunshe cikin wani rubutu da kwamandan Hisbah na jihar Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya wallafa a Shafinsa na Facebook.

Sheikh Daurawa ya bayyana cewa auren zai fi mayar da hankali ne ga marayu da kuma mutane masu ƙaramin ƙarfi, da nufin taimaka musu wajen gina rayuwar aure mai ɗorewa.

Kwamandan ya ƙara da cewa a cikin Shirin, kowanne ma’aurata za su samu cikakken tallafi, wanda ya haɗa da:

• Kayan ɗaki: gado, madubi, katifa, matasai da zanin gado

• Kayan abinci: shinkafa, taliya (spaghetti) da man girki

• Tufafi: zannuwan Ankara da hijabi ga mata; shadda da hula ga maza

• Sadaki: Naira 100,000 ga kowace amarya

• Tallafin sana’a: Naira 100,000 ga kowace mace domin fara ƙaramar sana’a

•Domin tabbatar da lafiyar masu niyyar shiga da kuma cancantarsu, za a gudanar da gwaje-gwajen lafiya, sannan masu nema za su cika fom guda uku na tantancewa.

Wannan shiri na nuna ƙudurin gwamnati wajen tallafa wa al’umma, rage talauci, da bunƙasa ci gaban jama’a.

Afrika, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
  • Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Isra’ila Zata Rusa Gidajen Da Suke Iyakarta Da Lebanon Labarai
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika
  • Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.