Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar
Published: February 5, 2026 at 10:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya yi Allah wadai da ƙaruwar hare-hare da kashe kashen da ake yi kwanan nan a sassan jihohin Kwara, Katsina da Benue, yana mai bayyana su a matsayin abin takaici, rashin hankali kuma cin zarafi kai tsaye ga al’ummar ƙasa baki ɗaya.

Wannan Allah wadai ya biyo bayan hare-haren da aka kai a ƙauyukan Woro da Nuku ne a Ƙaramar Hukumar Kaiama ta jihar Kwara, inda ake zargin ‘yan ta’adda sun kai hari a daren Talata da kisan aƙalla mutane 20 a ƙauyen Doma A da Doma B na Gundumar Tafoki, a Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina da kuma wani lamari na daban a ƙauyen Abande na gundumar Mbaikyor da Turan, a Ƙaramar Hukumar Kwande ta jihar Benue, inda aka ruwaito cewa an kashe mutane da dama.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matuƙar bakin ciki game da waɗánnan mummunan asarar rayuka na waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, yana mai miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da al’ummomin da abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin jihohin uku.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yabawa Gwamnonin jihohin Kwara, Katsina da Benue bisa jagoranci da jajircewarsu a duk lokacin da ake fuskantar ƙalubalen tsaro da ake yawan fuskanta, yana mai bayyana ƙoƙarinsu na tallafawa al’ummomin da abin ya shafa, da ƙarfafa tsarin tsaro a yankin da kuma haɗa kai da hukumomin tarayya don farfaɗo da zaman lafiya.

Ya yi ƙira ga hukumomin tsaron ƙasar su ƙara himma wajen tattara bayanan sirri, da sanya ido da kuma ɗaukar matakan da suka dace na gano waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma waɗanda ke tallafa musu, yana mai jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyi babban alhakin ne dake kan duk wani shugaba.

“Ƙungiyar Gwamnonin Arewa tana goyon bayan hukumomin tsaronmu kuma tana ƙira a garesu, su ɗauki duk wani matakin daya dace don gurfanar da masu laifin a gaban shari’a. Bai kamata masu aikata waɗannan laifukan su sha ba tare da hukunci ba,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin na Arewa ya tabbatarwa ‘yan Najeriya jajircewar Ƙungiyar ta yi na yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya, da hukumomin tsaro, da masarautun gargajiya da shugabannin al’umma don magance matsalolin rashin tsaro ta hanyar haɗakar matakan tsaro masu ƙarfi, da tattara bayanan sirri da leƙen asiri da kuma samar da tallafi a harkokin tattalin arziƙi da zamantakewa na dogon lokaci.

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka mutu, sannan ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya baiwa waɗanda suka ji rauni sauƙi, yayin da ya yi ƙira ga ‘yan ƙasar da su ci gaba da kasancewa cikin shiri tare da yin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro don daƙile aika-aikar ta’addanci.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka.
Next Post: Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.