Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar
Published: February 5, 2026 at 10:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya yi Allah wadai da ƙaruwar hare-hare da kashe kashen da ake yi kwanan nan a sassan jihohin Kwara, Katsina da Benue, yana mai bayyana su a matsayin abin takaici, rashin hankali kuma cin zarafi kai tsaye ga al’ummar ƙasa baki ɗaya.

Wannan Allah wadai ya biyo bayan hare-haren da aka kai a ƙauyukan Woro da Nuku ne a Ƙaramar Hukumar Kaiama ta jihar Kwara, inda ake zargin ‘yan ta’adda sun kai hari a daren Talata da kisan aƙalla mutane 20 a ƙauyen Doma A da Doma B na Gundumar Tafoki, a Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina da kuma wani lamari na daban a ƙauyen Abande na gundumar Mbaikyor da Turan, a Ƙaramar Hukumar Kwande ta jihar Benue, inda aka ruwaito cewa an kashe mutane da dama.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matuƙar bakin ciki game da waɗánnan mummunan asarar rayuka na waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, yana mai miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da al’ummomin da abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin jihohin uku.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yabawa Gwamnonin jihohin Kwara, Katsina da Benue bisa jagoranci da jajircewarsu a duk lokacin da ake fuskantar ƙalubalen tsaro da ake yawan fuskanta, yana mai bayyana ƙoƙarinsu na tallafawa al’ummomin da abin ya shafa, da ƙarfafa tsarin tsaro a yankin da kuma haɗa kai da hukumomin tarayya don farfaɗo da zaman lafiya.

Ya yi ƙira ga hukumomin tsaron ƙasar su ƙara himma wajen tattara bayanan sirri, da sanya ido da kuma ɗaukar matakan da suka dace na gano waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma waɗanda ke tallafa musu, yana mai jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyi babban alhakin ne dake kan duk wani shugaba.

“Ƙungiyar Gwamnonin Arewa tana goyon bayan hukumomin tsaronmu kuma tana ƙira a garesu, su ɗauki duk wani matakin daya dace don gurfanar da masu laifin a gaban shari’a. Bai kamata masu aikata waɗannan laifukan su sha ba tare da hukunci ba,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin na Arewa ya tabbatarwa ‘yan Najeriya jajircewar Ƙungiyar ta yi na yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya, da hukumomin tsaro, da masarautun gargajiya da shugabannin al’umma don magance matsalolin rashin tsaro ta hanyar haɗakar matakan tsaro masu ƙarfi, da tattara bayanan sirri da leƙen asiri da kuma samar da tallafi a harkokin tattalin arziƙi da zamantakewa na dogon lokaci.

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka mutu, sannan ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya baiwa waɗanda suka ji rauni sauƙi, yayin da ya yi ƙira ga ‘yan ƙasar da su ci gaba da kasancewa cikin shiri tare da yin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro don daƙile aika-aikar ta’addanci.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka.
Next Post: Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.