Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Published: January 13, 2026 at 11:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar Gombe ta fara duba lafiyar masu niyyar zuwa aikin Hajji na shekarar 2026 a Asibitin kwarerru na jihar Gombe.

An shirya wannan Duba lafiyar ne domin tantance halin lafiyar masu niyyar tafiya kasa mai tsarki ta Saudiyya, kafin a fara tafiya.

Da yake magana a wajen kaddamar da aikin duba lafiyar, Sakataren hukumar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya bayyana cewa duba lafiyar wajibi ne, kuma yana daga cikin manyan sharuddan da ake buƙata kafin a fitar da bizar Hajji ga masu niyya.

Alhaji Sa’adu ya ƙara da cewa an kammala duk shirye-shiryen da suka dace tare da shugabancin Asibitin domin tabbatar da cewa aikin zai gudana lafiya ba tare da wata matsala ba.

Ya lura cewa duba lafiyar bana ya fi na shekarun baya zurfi, domin yana kunshe da gwaje-gwaje na mahimman sassan jiki, ciki har da na zuciya, domin tabbatar da cewa duk wanda zai tafi Hajji yana da ƙoshin lafiya.

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Lafiya na Asibitin kwarerru na Gombe, Dr. Sambo Dawa, ya tabbatar da cewa dukkanin masu niyyar Hajji za su samu cikakken duba lafiya daga ƙwararrun ma’aikatan lafiya.

Dr. Dawa ya ce asibitin ya tanadi kayan aiki da ma’aikatan da suka dace domin gudanar da aikin yadda ya kamata bisa ka’idojin lafiya na ƙasa da ƙasa.

Wannan duba lafiyar zai taimaka wajen kare lafiyar alhazan jihar Gombe yayin aikin Hajjin 2026.

Kiwon Lafiya

Post navigation

Previous Post: Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya
Next Post: Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
Gwamnatin Tinubu Ta Warware Basussukan Fansho Na Shekaru 18 Afrika
Kaduna: Masana Sun Nemi A Sauya Tsohon Wurin Zubar Da Shara Na Tudun-Ilu Afrika
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Arsenal Ta Fara Kare Kambun Gasar Premier League Da Ci 3-0 A Kan Coventry City Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.