Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro
Published: February 6, 2026 at 8:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasar Afirka ta kudu ta sanar da samun allurar rigakafi na farko cikin shekaru 20 kan cutar boro, (foot and mouth disease) a turance, yayin da take neman bunkasa sarrafa maganin rigakafin a cikin gida, don tunkarar barkewar annobar mafi muni a shekaru masu yawa.

Cutar boro, cuta ce da ake saurin dauka, Wadda kuma Shanu zasu iya kamuwa da ita.

Tana sa kuraje a baki da kofato masu radadi da ciwo. Duk da cewa bata fiye jawo mutuwar shanun ba, amma tana dakile amfanin da ake samu daga dabbobin, kama da haihuwa ko samun madara.

Rigakafin, wadda hukumar binciken aikin noma ta Afirka ta Kudu ta samar, wani bangare ne na kudurin da kasar ke da shi na yiwa kashi 80 cikin 100 na shanun ta da suka kai kimanin miliyan 12 allura.

Hukumar zata rika samar da allurai 20,000 kowanne mako, daga watan Maris na wannan shekarar, har ta kara wa’adin zuwa 200,000 a shekarar 2027.

Afrika, Kiwon Lafiya

Post navigation

Previous Post: Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya
Next Post: Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India Najeriya
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.