Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka
Published: February 6, 2026 at 8:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araqchi ya ce tattaunawar da ake tsakanin kasar sa da Amurka a Oman, inda Oman din ta zama me sulhuntawa, ya fara da nasara, kuma yana sa ran za’a dore a haka, a wani furuci da yayi da zai taimaka wajen kawar da fargabar da ake yi na cewa rashin cimma yarjejeniya zai iya tsunduma gabas ta tsakiya barkewar yaki.

Sai dai kuma ministan yace bayan tattaunawar a Muscat, babban birnin kasar Oman, suna bukatar duk wata ganawa Ayi ta ba tare da barazana ko matsin lamba ba. Ya ce Tehran zatayi magana ne kawai kan makamanta na nukiliya, ba zata yi magana kan wani abu ba kuma da Amurka.

Yayin da duka bangarorin biyu suka amince da farfado da huldar diplomasiyya tsakanin su kan takaddamar da ke tsakanin Iran da kasashen yamma game da makaman ta na nukiliya, fadar Washington ta so ta fadada tattaunawar zuwa makamai masu linzami da Iran din ta mallaka. Su kuma hukumomin Iran sun ce baza su tattauna kan hakan ba.

Afrika, Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro
Next Post: Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi

Karin Labarai Masu Alaka

Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
  • Hamas Ta Kwance Damara Afrika
  • Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.