Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Published: December 5, 2025 at 7:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Shugaba Donald Trump na Amurka ya hada kan shugabannin Kwango ta Kinshasa da Rwanda domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya jiya alhamis birnin Washington, duk da cewa har yanzu ana can ana ci gaba da gwabza fada a yankin da ya jima yana fama da fitina.

Shugaba Paul Kagame na Rwanda da shugaba Felix Tshisekedi na Kwango sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin kan tattalin arziki da aka cimma a watan da ya shige, da kuma yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka da Qatar suka kulla tsakanin sassan biyu a watan Yuni.

Har ila yau an shirya cewa zasu sanya hannu a kan wata yarjejeniyar game da muhimman ma’adinai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ta bawa shugaba Donald Trump na Amurka wata sabuwar nasarar da aka ce ba ta zahiri ba, a kokarinsa na nuna cewa shi mai kokarin wanzar da zaman lafiya ne, a wannan karon a saboda har yanzu ana zub da jini a wannan yakin da aka ce an rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshensa.

Amurka tana kwadayin sanya hannunta a kan ma’adinai masu muhimmanci da yawa da kasar Kwango take da su, kuma tana ta kokarin dakile fintinkau da kasar China ta yi a fannin samo irin wadannan ma’adinai a fadin duniya.

A yayin da shugabannin kasashen biyu ke rattaba hannu a kan wannan yarjejeniya, an bada rahoton gumurzu a tsakanin’yan tawayen kungiyar M23 da Rwanda ke goyon baya da sojojin gwamnatin Kwango a lardin Kivu ta Kudu.

Wani kakakin kungiyar M23 ya zargi sojojin gwamnati da laifin cilla bama bamai a kan yankunan fararen hula.

Masu fashin baki sun ce tsoma bakin Amurka a cikin lamarin ya dakile yaduwar fadan, amma kuma bai iya warware muhimman batutuwan da suka janyo wannan yakin ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Next Post: Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi

Karin Labarai Masu Alaka

Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.