Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Published: December 5, 2025 at 7:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Shugaba Donald Trump na Amurka ya hada kan shugabannin Kwango ta Kinshasa da Rwanda domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya jiya alhamis birnin Washington, duk da cewa har yanzu ana can ana ci gaba da gwabza fada a yankin da ya jima yana fama da fitina.

Shugaba Paul Kagame na Rwanda da shugaba Felix Tshisekedi na Kwango sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin kan tattalin arziki da aka cimma a watan da ya shige, da kuma yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka da Qatar suka kulla tsakanin sassan biyu a watan Yuni.

Har ila yau an shirya cewa zasu sanya hannu a kan wata yarjejeniyar game da muhimman ma’adinai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ta bawa shugaba Donald Trump na Amurka wata sabuwar nasarar da aka ce ba ta zahiri ba, a kokarinsa na nuna cewa shi mai kokarin wanzar da zaman lafiya ne, a wannan karon a saboda har yanzu ana zub da jini a wannan yakin da aka ce an rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshensa.

Amurka tana kwadayin sanya hannunta a kan ma’adinai masu muhimmanci da yawa da kasar Kwango take da su, kuma tana ta kokarin dakile fintinkau da kasar China ta yi a fannin samo irin wadannan ma’adinai a fadin duniya.

A yayin da shugabannin kasashen biyu ke rattaba hannu a kan wannan yarjejeniya, an bada rahoton gumurzu a tsakanin’yan tawayen kungiyar M23 da Rwanda ke goyon baya da sojojin gwamnatin Kwango a lardin Kivu ta Kudu.

Wani kakakin kungiyar M23 ya zargi sojojin gwamnati da laifin cilla bama bamai a kan yankunan fararen hula.

Masu fashin baki sun ce tsoma bakin Amurka a cikin lamarin ya dakile yaduwar fadan, amma kuma bai iya warware muhimman batutuwan da suka janyo wannan yakin ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Next Post: Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi

Karin Labarai Masu Alaka

An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.