Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Published: December 5, 2025 at 7:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Shugaba Donald Trump na Amurka ya hada kan shugabannin Kwango ta Kinshasa da Rwanda domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya jiya alhamis birnin Washington, duk da cewa har yanzu ana can ana ci gaba da gwabza fada a yankin da ya jima yana fama da fitina.

Shugaba Paul Kagame na Rwanda da shugaba Felix Tshisekedi na Kwango sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin kan tattalin arziki da aka cimma a watan da ya shige, da kuma yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka da Qatar suka kulla tsakanin sassan biyu a watan Yuni.

Har ila yau an shirya cewa zasu sanya hannu a kan wata yarjejeniyar game da muhimman ma’adinai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ta bawa shugaba Donald Trump na Amurka wata sabuwar nasarar da aka ce ba ta zahiri ba, a kokarinsa na nuna cewa shi mai kokarin wanzar da zaman lafiya ne, a wannan karon a saboda har yanzu ana zub da jini a wannan yakin da aka ce an rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshensa.

Amurka tana kwadayin sanya hannunta a kan ma’adinai masu muhimmanci da yawa da kasar Kwango take da su, kuma tana ta kokarin dakile fintinkau da kasar China ta yi a fannin samo irin wadannan ma’adinai a fadin duniya.

A yayin da shugabannin kasashen biyu ke rattaba hannu a kan wannan yarjejeniya, an bada rahoton gumurzu a tsakanin’yan tawayen kungiyar M23 da Rwanda ke goyon baya da sojojin gwamnatin Kwango a lardin Kivu ta Kudu.

Wani kakakin kungiyar M23 ya zargi sojojin gwamnati da laifin cilla bama bamai a kan yankunan fararen hula.

Masu fashin baki sun ce tsoma bakin Amurka a cikin lamarin ya dakile yaduwar fadan, amma kuma bai iya warware muhimman batutuwan da suka janyo wannan yakin ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Next Post: Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi

Karin Labarai Masu Alaka

Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
  • Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.