Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Published: December 5, 2025 at 7:27 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Rundunar sojojin Amurka ta ce ta kai hari a kan wani karamin jirgin ruwan da ake zargin na safarar muggan kwayoyi ne a yankin ruwa na kasa da kasa a gabashin tekun Pacific jiya alhamis, ta kashe mutane hudu.

Rundunar sojojin ta Amurka, ta fada cikinwata sanarwar da ta bayar a dandalin sada zumunta na X cewa bayanan leken asiri sun tabbatar da cewa jirgin ruwan yana dauke da muggan kwayoyi, kuma an kai masa hari a kan hanyar da masu safarar muggan kwayoyi suka saba bi a gabashin tekun Pacific.

A halin da ake ciki, ‘yan majalisar dokokin Amurka sun samu ganin takardar dake kunshe da takaitaccen bayani da ya tsara matakan da gwamnatin Trump take dauka na kai hari kan jiragen ruwan da ake zargin suna dauke da kwayoyi a tekun Pacific.

‘Yan majalisar suna daukar wannan takarda a zaman mai muhimmanci ga binciken da suke yi na wani harin da sojojin Amurka suka kai kan wani jirgin a ranar 2 ga watan Satumba, inda suka kashe mutane 11, cikinsu har da wasu mutane biyu da suka kubuta da rai daga harin farko da aka kai kan jirgin.

Wannan takardar da ta takaita bayanin tana dauke da shafuka biyu, kuma ta zayyana jerin masu bayarda umurni, da yadda gwamnatin Trump take amfani da bnayanan leken asiri wajen gano irin wadannan jirage.

‘Yan majalisar sun bukaci da a kawo musu cikakkiyar takardar wadda ke dauke da bayanin komai da komai game da hare-haren, amma ba a san ko ma’aikatar tsaro zata yarda su gani ba.

A halin da ake ciki dai, manyan ‘yan jam’iyyar Democrat a majalisar dokoki dake cikin wadanda aka yi ma bayanin wasu hare-haren da aka kai a tekun Caribbean sun fada jiya alhamis cewa hankulansu sun tashi da bidiyon da suka gani na wasu mutane biyu da suka kubuta da rai, amma sai aka kara kai musu hari aka kashe su, Sai dai kuma takwarorinsu na Republican sun kare wannan hari na biyu da cewa bai saba ma doka ba.

Babban dan jam’iyyar Democrat a kwamitin kula da ayyukan leken asiri a majalisar wakilai, Jim Himes yace sun ga mutane biyu wadanda ba su da wata hanyar da zasu iya zuwa wani wuri, da jirginsu da aka gama lalatawa, amma sai aka kashe su.

Yace wannan abu na daya daga cikin abubuwa mafi tashin hankali da ya gani.

Shi ma babban dan Demicrat a kwamitin kula da ayyukan soja na majalisar dattijai, Jack Reed, yace hankalinsa ya tashi matuka da wannan bidiyo da ya gani kuma ya kamata a sake shi jama’a su gani.

Amma kuma shugaban kwamitin ayyukan leken asiri na majalisar dattijai dan jam’iyyar Republican, Tom Cotton, cewa yayi shi abinda ya gani mutanen biyu suna kokarin su juya jirginsu da ya kife ne, dauke da muggan kwayoyi zuwa Amurka domin su ci gaba da fafatawa.

Amurka

Post navigation

Previous Post: CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya
Next Post: Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Sake Fasalin Shirin NYSC Afrika
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.