Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 11, 2026 at 4:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Da yai magana kan rikicin na gabas ta tsakiya, shugaban majalisar tarayyar turai, Antonio Costa, ya fada ranar talata cewa Rasha ce take cin ribar yakin da ake yi a gabas ta tsakiya, ganin farashin mai ya tashi, kuma ya kauda hankali daga yakin da take da Ukraine.

“Zuwa yanzu dai kasa daya ce ta sami nasarar wannan yaki,” itace Rasha, Costa ya fada a wani jawabi da yayi wa jakadun Kungiyar tarayyar turai.

Antonio Costa, ya jaddada bukatar kungiyar tarayyar turai ta kare tsarin duniya na bin doka da oda, wadda yace ahalin yanzu Amurka take yi wa kalubale, daga nan ya shawarwaci duka sassa a rikicin na gabas ta tsakiyya, su koma teburin shawarwari.

Ahalinda ake ciki kuma, farashin mai ya fadi da kamar kashi 15 cikin dari ranar talata, kwana daya bayanda mai yayi tashin goron zabbi, rabon da ya kai haka tun 2022, faduwar farashin ya biyo bayan kalaman shugaban Amurka Trump cewa yakin ya kusa zuwa karshe.

Yau mai da ake kira Brent ana cinikinsa kan dala 84 da centi 73 kan ko wani gangar danyen mai, yayinda wadda ake kira West Texas shi kuma ya tashi kan dala 80 da centi 31. Farashin ya kara faduwa, bayan da ministan makamashi na Amurka Chris Wright ya rubuta a shafinsa na X cewa, sojojin Amurka sun taimaka an wuce da mai ta mashigan ruwa na Hormuz.

Wannan lamari na tsadar mai yana kalubale ga rinjayen da jam’iyyar Republican take dashi a zaben rabin wa’adi mai zuwa, kamar dai yadda masu nazarin harkokin yau da kullum suke hasashe.

Har yanzu dai kan yakin na gabas ta tsakiya, Australia zata tura jirgin leken asiri zuwa gabas ta tsakiya, kuma zata aike da makamai masu linzami zuwa hadaddiyar daular larabawa, amma ba zata tura sojojinta na kasa zuwa Iran ba, PM kasar Anthony Albanese ya fada a ranar talata.

Albanese yace, taimakon da Australia take da kayan yaki, zai taimakawa kasashe da suke yankin Gulf su kare kan su daga hare hare daga Iran ba babu hujja.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Next Post: Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe Afrika
APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
  • Yayale Ahmed Ya Jagoranci Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaron Arewa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.