Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Published: March 11, 2026 at 4:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sunyi luguden wuta kan Iran a jiya talata, da ma’aikatar tsaron Amurka da ake kira Pentagon da Farisawan suka ce shine hari mafi tsanani tun fara yakin, duk da tsammanin da kasuwannin sayar da hannayen jari na duniya suka yi cewa shugaba Donald Trump zai kawo karshen yakin bada jumawa ba.

Kara jawo kalubale ga tattalin arzikin duniya, rundunar juyin juya hali ta Iran tace zata hana jigilar mai daga yankin Gulf idan Amurka da Isra’ial basu tsaida kai mata hari ba.

Sakataren ma’aikatar Tsaron Amurka Pete Hegseth yace “yau zata kasance rana da muka fi tsananta kai hare hare a cikin Iran, jiragen yaki mafi yawa, tare da amfani da bayanan sirri mai inganci,” inji sakataren a wani taro da manema labarai.

Mazauna birnin Tehran da suka yi magana da kamfanin dilancin labarai na Reuters bisa sharadin ba za’a bayyana sunayen su ba, suka ce babu inda jiragen yakin suka bari a birnin Tehran. Tace sai ka dauka jahannama. Tace ‘yayanta har tsoron bacci suke yi.

Duk da haka, kalaman shugaba Trump ranar Litinin cewa, “kusan an kammala yakin,” masu zuba jari sunyi amannar yakin zai kare nan ba da jumawa ba, kamin kassarawar da aka yi wa jigilar makamashi ta durkusar da tattalin arzikin duniya.

Shugabannin Iran suna ci gaba da nuna turjiya ko a yau talata. “Hakika bama neman a tsagaita wuta, mun hakikance cewa tilas a kwabi bakin mai tsaukana, saboda su koyi darasi, har abada ba za su kaiwa Iran hari ba, inji a kakakin majaisar dokokin kasar, Mohammmed Baqer Qalibaf, a shafinsa na X.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran
Next Post: Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.