Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma
Published: December 8, 2025 at 4:42 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A karon farko tun bayan da gwamnatin Nijar ta kudiri aniyar maka kamfanin Orano a kotu, kungiyoyin farar hula a kasar sun jaddada goyon baya kan abin da suka kira yunkurin kwato ‘yancin a kan sha’anin ma’adanai.
Kungiyoyin sun kuma shawarci hukumomin na Nijar da su janye lasisin hakar zinare daga hannun kamfanonin da suka yi kaka-gida don mayar da komai a hannun ‘yan kasa.
A wata sanarwar da ta fitar ne kungiyar M62 ta bayyana matsayinta dangane da kace nacen da ya taso a tsakanin hukumomin Nijar, da kamfanin Orano na Faransa bayan da Nijar ta fara kwashe ton ton na Uranium din da ke jibge shekaru sama da biyu a garin Arlit.
Kungiyar tace ta na goyon matakin da gwamnatin Nijar ta dauka, wanda ta ke ganinsa tamkar matakin kawo karshen mulkin mallakar da aka shafe shekaru fiye da 60 a na yi wa kasar harakar Uranium. Falmata Taya na daga cikin shugabanin M62.
Ita ma kungiyar FRSA mai da’awar kwato ‘yancin kai Afirka a sanarwar da ta bayar ta bayyana gamsuwa da abin da ta kira sabon babin da gwamnatin Abdourahamane Tiani ta bude a fannin ma’adanan karkashin kasa. Salissou Ibrahim shine sakataren watsa labaran kungiyar.
Ko baya ga harakar Uranium kungiyar M62 na ganin bukatar gwamnatin Nijar ta fadada sauye sauyen da ta fara zuwa sha’anin hakar zinare.
Mahawwara kan hurumin fitar da Uranium zuwa waje a tsakanin gwamnatin Nijar da kamfanin Orano na Faransa na ci gaba da karfafa ne a wani lokacin da bangarorin biyu ke jiran hukuncin kotun CIRDI dangane da makomar ton 1300 na Uranium da ke girke a yankin arewacin Nijar.
M62 ta bukaci hukumomin kasar su gudanar da bincike kan illahirin aiyukan bankin duniya saboda alakarsu da kotun CIRDI.
Afrika

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Next Post: “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.