Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma
Published: December 8, 2025 at 4:42 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A karon farko tun bayan da gwamnatin Nijar ta kudiri aniyar maka kamfanin Orano a kotu, kungiyoyin farar hula a kasar sun jaddada goyon baya kan abin da suka kira yunkurin kwato ‘yancin a kan sha’anin ma’adanai.
Kungiyoyin sun kuma shawarci hukumomin na Nijar da su janye lasisin hakar zinare daga hannun kamfanonin da suka yi kaka-gida don mayar da komai a hannun ‘yan kasa.
A wata sanarwar da ta fitar ne kungiyar M62 ta bayyana matsayinta dangane da kace nacen da ya taso a tsakanin hukumomin Nijar, da kamfanin Orano na Faransa bayan da Nijar ta fara kwashe ton ton na Uranium din da ke jibge shekaru sama da biyu a garin Arlit.
Kungiyar tace ta na goyon matakin da gwamnatin Nijar ta dauka, wanda ta ke ganinsa tamkar matakin kawo karshen mulkin mallakar da aka shafe shekaru fiye da 60 a na yi wa kasar harakar Uranium. Falmata Taya na daga cikin shugabanin M62.
Ita ma kungiyar FRSA mai da’awar kwato ‘yancin kai Afirka a sanarwar da ta bayar ta bayyana gamsuwa da abin da ta kira sabon babin da gwamnatin Abdourahamane Tiani ta bude a fannin ma’adanan karkashin kasa. Salissou Ibrahim shine sakataren watsa labaran kungiyar.
Ko baya ga harakar Uranium kungiyar M62 na ganin bukatar gwamnatin Nijar ta fadada sauye sauyen da ta fara zuwa sha’anin hakar zinare.
Mahawwara kan hurumin fitar da Uranium zuwa waje a tsakanin gwamnatin Nijar da kamfanin Orano na Faransa na ci gaba da karfafa ne a wani lokacin da bangarorin biyu ke jiran hukuncin kotun CIRDI dangane da makomar ton 1300 na Uranium da ke girke a yankin arewacin Nijar.
M62 ta bukaci hukumomin kasar su gudanar da bincike kan illahirin aiyukan bankin duniya saboda alakarsu da kotun CIRDI.
Afrika

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Next Post: “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.