Hukumar Jin Dadin Alhazain Najeriya wato (NAHCON) ta ƙaddamar da gagarumin rukunin asibitoci a birnin Madina, domin tabbatar da lafiyar maniyyata a yayin aikin Hajjin bana.
Asibitin ya ƙunshi sashen jiyya na maza da mata, dakin shan magani (Pharmacy), sashen kula da gaggawa (OPD), da kuma dakin likitoci da nas-nas.
An shirya asibitin ne domin bai wa maniyyata ‘yan Najeriya damar samun magunguna da duba lafiya ba tare da biyan ko sisi ba. Tuni dai an fara duba mahajjata a bangarori daban-daban na asibitin.
Wannan mataki dai na zuwa ne daidai lokacin da dubun-dubatar maniyyata daga Najeriya suka fara isa kasar Saudiyya domin sauke farali.


