Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani
Published: December 15, 2025 at 4:18 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Matasa a birnin Kano sun kashe wani matashi da ake zargi da kisan ladanin wani masallaci a Unguwar Hotoro dake birnin Kano, arewa maso yammacin Najeriya.

Lamarin ya faru ne a unguwar Hotoro, inda bayanai suka tabbatar da cewa matashin ya yi wa ladanin, mai suna Zubairu Kasim, yankar rago ne da asubahin ranar Litinin sa’ilin da yake shirin kiran sallar asubahi.

Lokacin da manema labarai suka isa inda abin ya faru, sun iske ƴan’uwa da sauran al’ummar unguwar na zaman makoki bayan jana’izar ladanin.

A lokacin da ya tattauna da ‘yan jarida, ɗan mamacin, Isa Kasim, ya ce: “Da asuba ne mahaifina ya fita kiran sallah, inda ya yi kira na farko sai ya zauna yana ɗan lazimi kafin ya yi kira na biyu kawai, Sai wani ya shiga cikin masallacin da makami, ya kama mahaifina ya danne shi ya masa yankan rago, a taƙaice dai ya cire masa maƙogaro.”

Bayan faruwar haka ne wasu daga cikin matasan unguwar suka taru suka hallaka matashin da ya kashe ladanin.

Isa Kasim ya ƙara da cewa: “Allah ya yi shi ma wanda ya kai harin ba zai tsira ba, ƴan unguwa suka taru har suka cimma wanda ya kashe shi, inda suka kashe shi, shi ma.”

Ya ƙara da cewa “Bayan da ƴan unguwa suka kashe wanda ya kai harin, sai su ka ga maƙogwaron mahaifina a cikin aljihunsa a leda.”

Hukumomi sun tura jami’an tsaro unguwar domin tabbatar da doka da oda bayan ɗan yamutsin da aka samu.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane
Next Post: AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya

Karin Labarai Masu Alaka

An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.