Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe
Published: December 6, 2025 at 8:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a ayyukan masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu a fadin jihar.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar dauke da sahannun Jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Buhari Abdullah, an kama Abdullahi Ibrahim mai shekaru 40 a garin Tilde dake karamar hukumar Funakaye, a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, bayan samun sahihan bayanai daga wani mai kishin kasa da suka zargeshi da boye masu laifi.

A yayin bincike, Abdullahi ya amsa laifin sa, inda ya bayyana cewa yana da hannu a satar shanu da kuma wasu hare haren masu garkuwa da mutane a fadin jihar Gombe.

Haka kuma ya fadi sunayen wasu abokan aikin sa da suka hada kai wajen gudanar da miyagun ayyukan a jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da jihar Adamawa.

Rundunar ta ce a bisa wannan bayani ne jami’an ‘yan sanda da ke Operation Hattara tare da hadin gwiwar kungiyar masunta na jihar Gombe suka kai samame a wasu maboyar miyagun, inda aka yi musayar wuta da suka kai ga cafke karin mutum shida.

Wadanda aka kama sun hada da, Usman Mohammed, mai shekaru 30,Hussain Idris, mai shekaru 37, Adamu Tukur, mai shekaru 37 ,Yau Abdullahi, mai shekaru 25 da Ali Umar, mai shekaru 18 sai Hassan Usman, mai shekaru 40 da kuma Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40, daga Tilde,Karamar Hukumar Funakaye jihar Gombe

Sannan Rundunar ta tabbatar da ci gaba da gudanar da bincike tare da shirin gurfanar da su a gaban kotu.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026.
Next Post: Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA.

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.