Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe
Published: December 6, 2025 at 8:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a ayyukan masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu a fadin jihar.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar dauke da sahannun Jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Buhari Abdullah, an kama Abdullahi Ibrahim mai shekaru 40 a garin Tilde dake karamar hukumar Funakaye, a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, bayan samun sahihan bayanai daga wani mai kishin kasa da suka zargeshi da boye masu laifi.

A yayin bincike, Abdullahi ya amsa laifin sa, inda ya bayyana cewa yana da hannu a satar shanu da kuma wasu hare haren masu garkuwa da mutane a fadin jihar Gombe.

Haka kuma ya fadi sunayen wasu abokan aikin sa da suka hada kai wajen gudanar da miyagun ayyukan a jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da jihar Adamawa.

Rundunar ta ce a bisa wannan bayani ne jami’an ‘yan sanda da ke Operation Hattara tare da hadin gwiwar kungiyar masunta na jihar Gombe suka kai samame a wasu maboyar miyagun, inda aka yi musayar wuta da suka kai ga cafke karin mutum shida.

Wadanda aka kama sun hada da, Usman Mohammed, mai shekaru 30,Hussain Idris, mai shekaru 37, Adamu Tukur, mai shekaru 37 ,Yau Abdullahi, mai shekaru 25 da Ali Umar, mai shekaru 18 sai Hassan Usman, mai shekaru 40 da kuma Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40, daga Tilde,Karamar Hukumar Funakaye jihar Gombe

Sannan Rundunar ta tabbatar da ci gaba da gudanar da bincike tare da shirin gurfanar da su a gaban kotu.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026.
Next Post: Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA.

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika
  • Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
  • Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.