Kasar Chadi ta rufe iyakar ta da kasar Sudan a yau Litinin, bayan da yakin basasar da ake tafkawa tsakanin rundunar sojin Sudan da dakarun tawaye na RSF, yayi sanadiyar hallaka sojojin Chadi 5, a cewar wasu majiyoyi biyu da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Yakin da ake ta tafkawa tun a watan Aprilun shekara ta 2023 tsakanin bangarorin biyu a Sudan, na shafar bangaren kasar Chad, lokaci zuwa lokaci, inda yake jawo salwantar rayuka da kuma lalacewar dukiya.
Gwamnatin Chadi ta ce za’a ci gaba da rufe iyakar kasar da Sudan har sai abinda hali yayi saboda irin mamaya da keta haddi da dakarun Sudan a duka bangarorin ke musu.


