Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa
Published: December 26, 2025 at 10:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jamhuriyar Nijar ta sanar da ɗaukar matakin ramuwar gayya ta haramta bai wa ’yan ƙasar Amurka biza gaba ɗaya, tare da hana shigowar ’yan ƙasar Amurka ƙasar Nijar na dindindin.

Wannan mataki na diflomasiyya mai ƙarfi ne, wanda ke da manyan tasiri ga dangantakar yankin da kuma hulɗar ƙasa da ƙasa.

Hakan ya biyo bayan sanarwar da Amurka tayi na dena bawa yan kasar Nijar bizar shiga Amurka, don haka shugabannin Nijar suka dauki matakin hana Amurkawa Shiga kasarsu

Kamfanin dillancin labarai na ANP ya ruwaito wata majiyar diflomasiyya na cewa ƙarƙashin dokokin gwamnatin Nijar babu wani ɗan Amurka da za a sake baiwa visa ta kowacce hanya haka zalika an haramtawa Amurkawa sanya ƙafa a cikin Nijar da sunan kowacce irin ziyara.

Majiyar diflomasiyyar ta ce mahukutan ƙasar ta Nijar ta umarci ma’aikatar harkokin wajen ƙasar da kada ta sake bayar da visa ga Amurkawa, matakin da ke nuna haramci na dindindin.

Majiyar ta bayyanawa kamfanin dillancin labarai na ANP cewa matakin na nuna cewa bazata duƙa ba, haka zalika ba zata zuba ido ga hukuncin na Amurka ba, maimakon haka za ta ɗauki mataki daidai da wanda Washington ta ɗauka.

A ranar 16 ga watan Disamba ne, Washington ta ƙara ƙasashe 7 ciki har da jamhuriyyar Nijar a jerin ƙasashen da za su fuskanci haramcin samun izinin shiga Amurka.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya
Next Post: Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
  • Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
  • ‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.