Wani Mai rike da sarautar gargajiya da wasu masana muhalli sun yi kira ga gwamnatin jihar Kaduna da ta gudanar da cikakken bincike kan tarin shara da ke tsoffin wuraren zubar da shara na jihar, waɗanda suka ce suna haddasa gurbacewar muhalli.
Sun kuma ba da shawarar mayar da wuraren zuwa shaguna na wucin gadi ko wasu abubuwan amfani ga al’umma domin samar da kuɗaɗen shiga, maimakon ci gaba da barin su suna haifar da gurbacewa da yaɗuwar cututtuka.
Shugaban Sashen Sadarwa da Dabaru na African Climate Reporters, kuma malami a African Institute of Waste Management and Environmental Studies, Malam Ibrahima Yakubu, ya kai ziyara wurin zubar da shara na Tudun-Ilu tare da wasu masana kimiyyar muhalli domin duba halin da wurin ke ciki da kuma tantance illolin da zai iya haifarwa ga muhalli da lafiyar al’ummar da ke zaune a kusa da wurin.
Wurin zubar da sharan Tudun-Ilu, wanda yake kusa da tashar kashe gobara da ke Tudun Wada a Jihar Kaduna, Arewa maso Yammacin Najeriya, na daga cikin tsofaffin wuraren zubar da shara a jihar.
Wurin ya jawo damuwa musamman saboda tasirinsa ga mazauna yankin, ciki har da mata da yara.
Bayan gudanar da binciken wurin, Ibrahima Yakubu da wasu masana kimiyyar muhalli sun bayyana cewa akwai buƙatar hukumomin da abin ya shafa su gudanar da cikakken tantancewar wurin tare da kwashe tarin sharan da ya yi yawa, domin kare mazauna yankin daga hayaki mai haɗari da ke fitowa daga wurin.
Ya kuma ba da shawarar a maye gurbin wurin da gine-gine kamar shaguna na wucin gadi da ’yan kasuwa za su yi amfani da su, ko kuma wasu abubuwan more rayuwa da za su amfani al’umma, maimakon barin robobi da sauran tarkace su ci gaba da taruwa suna gurbata muhalli.
Ya ce kwashe sharan zai taimaka wajen kare mazauna yankin daga hayaki da iskar gas mai guba da ke fitowa sakamakon kona shara da kuma ruɓewarta.
Mazauna Sun Koka Kan Hayaki da Illolin Lafiya
Wurin zubar da sharan yana cikin wata al’umma mai yawan jama’a, inda dubban mutane ke zaune a kewayen wurin.
Mazauna Tudun-Ilu sun sha yin kira ga hukumomin da abin ya shafa da su mayar da wurin zuwa wani wuri ko kuma su samar da ingantacciyar hanyar kula da sharan, suna bayyana damuwa kan hayaki da kuma yanayin wurin da ke shafar rayuwarsu ta yau da kullum.
Ibrahima Yakubu ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su daina cinna wa sharan wuta, tare da yin kira da a ƙara wayar da kan jama’a game da illolin kona shara a fili.
Da yake magana yayin ziyarar, shugaban al’ummar Unguwar Tudun-Ilu, inda wurin zubar da sharan yake, Mai Unguwa Mallam Husaini Yakubu, ya roƙi hukumomin da abin ya shafa da su kawo ƙarshen ci gaba da zubar da shara a wurin.
Ya ce mazauna yankin sun shafe shekaru suna fama da illolin wurin zubar da sharan, ciki har da hayaki mai ɗorewa da kuma matsalolin numfashi da ya ce suna addabar wasu daga cikin al’ummar.
A cewarsa, wurin ya ƙara zama wajen zubar da sharar dabbobi da kuma tarkacen da ake samu daga Kasuwar Kaduna ta Tsakiya, lamarin da ke haifar da hayaki da ke addabar al’ummar da ke kewaye da wurin, musamman daga safe har zuwa yamma.

Mai Unguwar ya ba da shawarar cewa hukumomi su yi la’akari da maye gurbin wurin da shaguna na wucin gadi ko wasu abubuwan amfani ga al’umma, domin kawo ƙarshen matsalolin muhalli da wurin ke haifarwa.
Ya kuma yi kira ga ƙungiyoyin agaji, ƙungiyoyin farar hula da masana harkokin lafiya da su haɗa kai da gwamnati da shugabannin al’umma wajen nemo mafita mai ɗorewa kan matsalar kula da shara a yankin.
Ya ƙara yin kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin masana muhalli, ’yan jarida, shugabannin al’umma, ƙungiyoyin farar hula da hukumomin gwamnati, domin tabbatar da cewa kula da shara ya zama babban abin da ake bai wa muhimmanci a faɗin birnin Kaduna.
Kira da a ɗauki Matakin Gaggawa
Masana sun yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kwashe tarin sharan, dakatar da kona shara a fili, samar da wuraren da suka dace don zubar da shara, tare da ƙarfafa tsarin tattara shara, sake sarrafa tarkace da kuma wayar da kan jama’a.
Sun ce irin waɗannan matakai za su taimaka wajen rage gurbacewar iska, inganta yanayin rayuwar mazauna yankin da kuma kare lafiyar jama’a a Tudun-Ilu da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da wurin.

A ƙarshe, Mai Unguwar ya yaba wa Ibrahima Yakubu da tawagar masana muhalli bisa lokacin da suka ware domin ziyartar yankin, tare da yin kira ga hukumomin da abin ya shafa da su ɗauki matakin da ya dace domin magance matsalar.


