Gwamnatin jihar Jigawa ta sake tabbatar da aniyarta na ci gaba da tallafa wa Cibiyar Bunƙasa Fasaha (Technology Incubation Centre – TIC) da ke Dutse domin bunƙasa kasuwancin fasaha, haɓaka harkokin kasuwanci da samar da ayyukan yi a faɗin jihar.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Manajan Cibiyar, Injiniya Shukuranu Uzairu, tare da tawagarsa a ziyarar girmamawa da suka kai masa a ofishinsa.
Dagaceri ya bayyana TIC Dutse a matsayin cibiyar da ta yi fice a jihar, inda ya yaba da irin gudunmawar da take bayarwa wajen bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire da tallafa wa masu sana’o’i da ‘yan kasuwa.
Ya ce gwamnatin jihar tana sane da irin ayyukan alheri da cibiyar ke yi wajen haɓaka sabbin dabarun kasuwanci, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da haɗa kai da ita domin ƙara faɗaɗa tasirinta wajen bunƙasa tattalin arziki.
Tun da farko, Manajan Cibiyar, Injiniya Shukuranu Uzairu, ya ce ziyarar na daga cikin shirin ƙarfafa alaƙa da masu ruwa da tsaki da kuma gano sabbin hanyoyin haɗin gwiwa tun bayan da ya karɓi ragamar jagorancin cibiyar.
Ya bayyana cewa shirin Cibiyoyin Bunƙasa Fasaha ya taka muhimmiyar rawa wajen haɓaka ƙirƙire-ƙirƙire da kasuwanci, yana mai cewa tallafin gwamnati ga irin waɗannan cibiyoyi a faɗin ƙasar ya taimaka wajen kafa dubban ƙanana da matsakaitan masana’antu (SMEs), tare da samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma a kaikaice.
Uzairu ya roƙi gwamnatin jihar da ta ƙara tallafa wa cibiyar ta hanyar bunƙasa kayayyakin more rayuwa, samar da wuraren masana’antu ga waɗanda suka kammala shirin koyon sana’a da matasa masu tasowa a harkokin kasuwanci, da kuma ƙarfafa sauran shirye-shiryen haɗin gwiwa domin faɗaɗa ayyukan cibiyar.
Ziyarar ta nuna ƙudirin Gwamnatin jihar Jigawa na amfani da fasaha, ƙirƙire-ƙirƙire da bunƙasa harkokin kasuwanci a matsayin hanyoyin inganta tattalin arziki da samar da ayyukan yi ga matasa.


