Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Published: January 3, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Amurka ta hambare gwanatin shugaba Maduro a Venezuela, kuma tace zata gudanar da harkokin kasar har zuwa lokacin da ya dace. Shugaban Amurka Donald Trump ne ya bayyana haka a wani taron da manema labarai a Mar-Largo, wurin shakatawarsa dake jihar Florida.

Da manema labarai suka matsa neman karin bayani kan yadda Amurka zata tafiyar da harkokin kasar ta Venezuela, shugaba Trump bai bada amsa kai tsaye ba. Yace “zamu tafiyarda harkokin kasar da gungun mutane. Kuma zamu tabbatar da cewa an tafiyar da kasar yadda ya kamata.” inji shugaban na Amurka.

Da ‘yan jarida suka matsa don jin yadda za’a aiwatar da shirin, shugaba Trump, yace “ana yin haka a halin yanzu.” Muna zabar mutane. Muna magana da mutane. Kuma za mu sanar da ku ko su wanene wadan nan mutanne, inji shugaba Trump.

Da yake magana a taron na manema labarai, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, yace, Maduro ba shine halataccen shugaban Venezuela ba. Domin tun a shekara ta 2020 zamanin gwamnatin Trump ta farko Amurka ta tuhumi Maduro, haka itama gwamnatin Biden da kuma gwamnatiin Trump ta yanzu.

A taro da manema labaran, shugaba Trump ya gargadi shugaban kasar Columbia cewa ya shiga taitayinsa. Yana zarginsa da sarrafawa da safarar miyagun kwayoyi,  Da aka tambayeshi gameda kasar Cuba, shugaba Trump, yace akwai bukatar ita ma Cuba a dubi lamarinta domin tana bukatar taimako.

Da suke maida martani kan wannan mataki, wakkilan majalisar dokokin Amurka ‘yan jam’iyyar Democrat, sunce jami’an gwamnati Trump basu gaya musu gaskiya ba a ganawarda suka yi da su a baya bayan nan gameda Venezuela, suko jami’an bangaren zartaswa sun fada musu basu da burin sauya gwamnati a Venezuela.

 

Amurka, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a
Next Post: Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.