Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Published: January 3, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Amurka ta hambare gwanatin shugaba Maduro a Venezuela, kuma tace zata gudanar da harkokin kasar har zuwa lokacin da ya dace. Shugaban Amurka Donald Trump ne ya bayyana haka a wani taron da manema labarai a Mar-Largo, wurin shakatawarsa dake jihar Florida.

Da manema labarai suka matsa neman karin bayani kan yadda Amurka zata tafiyar da harkokin kasar ta Venezuela, shugaba Trump bai bada amsa kai tsaye ba. Yace “zamu tafiyarda harkokin kasar da gungun mutane. Kuma zamu tabbatar da cewa an tafiyar da kasar yadda ya kamata.” inji shugaban na Amurka.

Da ‘yan jarida suka matsa don jin yadda za’a aiwatar da shirin, shugaba Trump, yace “ana yin haka a halin yanzu.” Muna zabar mutane. Muna magana da mutane. Kuma za mu sanar da ku ko su wanene wadan nan mutanne, inji shugaba Trump.

Da yake magana a taron na manema labarai, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, yace, Maduro ba shine halataccen shugaban Venezuela ba. Domin tun a shekara ta 2020 zamanin gwamnatin Trump ta farko Amurka ta tuhumi Maduro, haka itama gwamnatin Biden da kuma gwamnatiin Trump ta yanzu.

A taro da manema labaran, shugaba Trump ya gargadi shugaban kasar Columbia cewa ya shiga taitayinsa. Yana zarginsa da sarrafawa da safarar miyagun kwayoyi,  Da aka tambayeshi gameda kasar Cuba, shugaba Trump, yace akwai bukatar ita ma Cuba a dubi lamarinta domin tana bukatar taimako.

Da suke maida martani kan wannan mataki, wakkilan majalisar dokokin Amurka ‘yan jam’iyyar Democrat, sunce jami’an gwamnati Trump basu gaya musu gaskiya ba a ganawarda suka yi da su a baya bayan nan gameda Venezuela, suko jami’an bangaren zartaswa sun fada musu basu da burin sauya gwamnati a Venezuela.

 

Amurka, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a
Next Post: Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NEDC Ta Karyata Bada Tallafin Karatun MSc Da Ke Yawo A Kafafen Sadarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela Amurka
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.