Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela
Published: January 3, 2026 at 8:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Game da Hambarar da Mulkin Shugaban Kasar Venezuela Hukumomin duniya kuma, sunce “Wannnnan matakin ya kasance misali mai hadari, kan yadda za’a gudanar da al’amura nan gaba” inji kakakin sakataren MDD Antonio Gutierrez, ya ci gaba da cewa, sakataren na MDD yana jaddada muhimancin dukkan kasashen duniya su su mutunta dokokin kasa da kasa, ciki harda sharudda da dokokin MDD.

Mr. Gutierrez inji mai magana da yawunsa, yana nuna matukar damuwa cewa anan dai ba’a mutunta dokokin kasa da kasa ba.”

A nata bangaren Jamus ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Muna kira ga duk wadanda wannan lamari ya shafa, su gujewa ruruta wannan yanayi, kuma su nemi hanyoyin hannyoyin warware wannan batu ta fuskar siyasa,” Ta kara da cewa, Venezuela tana bukatar ko ta cancanci zaman lafiya, da tafarkin demokuradiyya nan gaba.”

China a nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Sin ta kadu, kuma tayi Allah wadai da kakkausar lafazi, amfani da karfin soja kan kasa mai ‘yanci, da kuma amfani da karfin soja kan shugaban kasa.”

Shi kuma da yake magana kan wannan lamari, ministan harkokin wajen Faransa yace, “matakin soja da ya kai ga kama shugaba Maduro, ya kaucewa amfani da karfi kamar yadda yake a dokokin kasa da kasa itama faransa ta sake jaddada cewa ba za’a samu zaman lafiya mai dorewa ba, idan aka tilasta shi daga ketare, Faransa tace ‘yan kasa ne kadai za su iya shata makomar su.

Da take magana kan wannan batu, ma’aikatar harkokin wajen Rasha tace, “A safiyar nan, Amurka ta nuna fin karfi ta amfani da karfin soja kan kasar Venezuela, wannan abun damuwa ne matuka, kuma abun Allah wadai ne.

Afirka ta kudu ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, ta bukaci kwamitin sulhu na MDD, yayi zaman gaggawa domin duba wannan lamari.

A kasashe dake Latin Amurka ra’ayoyi shugabannin kasashen sun sha ban ban, wasu suna Allah wadai da matakin, wasu kuma suna san barka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Next Post: Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
  • Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.