Mai Martaba Sarkin Gombe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan jihar Gombe, Alhaji (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar III, ya yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa abin da ya bayyana a matsayin shekaru bakwai na shugabanci mai cike da sauyi da ci gaba a fadin jihar Gombe.
Sarkin ya bayyana hakan ne yayin gaisuwar Sallah da Majalisar Masarautar Gombe ta kai wa gwamnan a gidan gwamnatin jihar da ke Gombe.

Da yake jawabi yayin ziyarar, Mai Martaban ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya cika alkawarin da ya dauka na aiki domin ci gaba da wadata a jihar, yana mai cewa nasarorin gwamnatin sun bayyana karara a muhimman fannoni da suka hada da gine-ginen more rayuwa, ilimi, lafiya, tsaro, bunkasa tattalin arziki, kare muhalli da kuma sabunta birane.
Ya bayyana shekaru bakwai na gwamnatin Inuwa Yahaya a matsayin lokaci na gagarumin sauyi da ci gaba mai dorewa a dukkan sassan jihar.
Sarkin ya yabawa gwamnatin kan kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro, yana mai cewa kafa Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ya taimaka wajen karfafa tsarin tsaro tare da tabbatar da Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya.
Haka kuma, Sarkin ya bayyana wasu daga cikin manyan ayyukan raya kasa da gwamnatin ta aiwatar da suka hada da yankin Three-Arms Zone, Muhammadu Buhari Industrial Park, Agro-Livestock Development Zone, katafaren mayanka na zamani, tashar Inland Dry Port, ayyukan magance zaizayar kasa, hanyoyi, fadada samar da ruwa, manyan makarantu da cibiyoyin lafiya.
Ya kuma yabawa gwamnatin kan shirye-shiryen sabunta birane da suka hada da gina Shehu Abubakar District da kuma gina gadar karkashin kasa ta farko a jihar, tare da ayyukan tsaftar muhalli da kawata birane.
Mai Martaban ya sake tabbatar da goyon bayan masarautar ga gwamnatin jihar tare da kira ga al’umma da su ci gaba da mara wa gwamnati baya domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da ci gaba.

Da yake nasa jawabin, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da bunkasa tattalin arziki da ci gaban al’umma a Jihar Gombe.
Gwamnan ya gode wa Sarkin da Majalisar Masarautar Gombe bisa ziyarar da kuma goyon bayan da suke bai wa gwamnatinsa, yana mai bayyana sarakunan gargajiya a matsayin muhimman abokan hulda wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a matakin al’umma.
Ya ce gwamnatinsa ta samu manyan nasarori cikin shekaru bakwai da suka gabata a fannoni daban-daban, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da amfani da albarkatun jihar yadda ya kamata domin inganta rayuwar jama’a.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jaddada cewa ci gaba aiki ne mai dorewa da ke bukatar hadin kai, fahimtar juna da goyon bayan jama’a baki daya.


