Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika

Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
Published: May 29, 2026 at 9:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 29, 2026

Mai Martaba Sarkin Gombe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan jihar Gombe, Alhaji (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar III, ya yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa abin da ya bayyana a matsayin shekaru bakwai na shugabanci mai cike da sauyi da ci gaba a fadin jihar Gombe.

Sarkin ya bayyana hakan ne yayin gaisuwar Sallah da Majalisar Masarautar Gombe ta kai wa gwamnan a gidan gwamnatin jihar da ke Gombe.

Da yake jawabi yayin ziyarar, Mai Martaban ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya cika alkawarin da ya dauka na aiki domin ci gaba da wadata a jihar, yana mai cewa nasarorin gwamnatin sun bayyana karara a muhimman fannoni da suka hada da gine-ginen more rayuwa, ilimi, lafiya, tsaro, bunkasa tattalin arziki, kare muhalli da kuma sabunta birane.

Ya bayyana shekaru bakwai na gwamnatin Inuwa Yahaya a matsayin lokaci na gagarumin sauyi da ci gaba mai dorewa a dukkan sassan jihar.

Sarkin ya yabawa gwamnatin kan kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro, yana mai cewa kafa Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida ya taimaka wajen karfafa tsarin tsaro tare da tabbatar da Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya.

Haka kuma, Sarkin ya bayyana wasu daga cikin manyan ayyukan raya kasa da gwamnatin ta aiwatar da suka hada da yankin Three-Arms Zone, Muhammadu Buhari Industrial Park, Agro-Livestock Development Zone, katafaren mayanka na zamani, tashar Inland Dry Port, ayyukan magance zaizayar kasa, hanyoyi, fadada samar da ruwa, manyan makarantu da cibiyoyin lafiya.

Ya kuma yabawa gwamnatin kan shirye-shiryen sabunta birane da suka hada da gina Shehu Abubakar District da kuma gina gadar karkashin kasa ta farko a jihar, tare da ayyukan tsaftar muhalli da kawata birane.

Mai Martaban ya sake tabbatar da goyon bayan masarautar ga gwamnatin jihar tare da kira ga al’umma da su ci gaba da mara wa gwamnati baya domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da ci gaba.

Da yake nasa jawabin, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da bunkasa tattalin arziki da ci gaban al’umma a Jihar Gombe.

Gwamnan ya gode wa Sarkin da Majalisar Masarautar Gombe bisa ziyarar da kuma goyon bayan da suke bai wa gwamnatinsa, yana mai bayyana sarakunan gargajiya a matsayin muhimman abokan hulda wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a matakin al’umma.

Ya ce gwamnatinsa ta samu manyan nasarori cikin shekaru bakwai da suka gabata a fannoni daban-daban, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da amfani da albarkatun jihar yadda ya kamata domin inganta rayuwar jama’a.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jaddada cewa ci gaba aiki ne mai dorewa da ke bukatar hadin kai, fahimtar juna da goyon bayan jama’a baki daya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.