Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Published: December 18, 2025 at 5:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya tabbatar da naɗin shugabannin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC)

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake naɗa sabon kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), biyo bayan tabbatar da su da Majalisar Dattawa ta yi a ranar 16 ga Disamba.

A cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, an bayyana cewa Dokta Mulisiu Olalekan Oseni ne sabon Shugaban Hukumar (Chairman), Dokta Oseni, wanda ya fara aiki a NERC a matsayin Kwamishina tun watan Janairun 2017, daga bisani ya riƙe muƙamin Mataimakin Shugaba, Naɗinsa a matsayin Shugaba ya fara aiki ne daga 1 ga Disamba, 2025, kuma zai ci gaba har zuwa cikar wa’adin sa na shekaru goma, kamar yadda Dokar Wutar Lantarki ta 2023 ta tanada.

Haka kuma, Dokta Yusuf Ali ya zama Mataimakin Shugaban Hukumar (Vice Chairman) kuma An fara naɗa shi a matsayin Kwamishina a watan Fabrairun 2022, kuma sabon muƙaminsa zai fara aiki daga 1 ga Disamba, 2025, har zuwa ƙarshen wa’adinsa na farko.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Nathan Rogers Shatti da Dafe Akpeneye, waɗanda dukkansu ke kan wa’adin su na biyu bayan an fara naɗa su a watan Janairun 2017, Haka kuma, Aisha Mahmud Kanti Bello na ci gaba da wa’adinta na biyu, bayan an fara naɗa ta a watan Disambar 2020.

A ɓangaren sababbin mambobi, Dokta Chidi Ike na kan wa’adinsa na farko tun bayan naɗinsa a watan Fabrairun 2022, yayin da Dokta Fouad Animashaun ya fara wa’adinsa na farko daga Disamba, 2025. Dokta Animashaun ƙwararren masani ne a fannin tattalin arzikin makamashi, kuma ya taɓa zama Babban Kwamishina kuma Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Legas.

Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin NERC da su ƙara ƙaimi wajen zurfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki a Nijeriya, tare da bin tanade-tanaden Dokar Wutar Lantarki ta 2023 gaba ɗaya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Next Post: Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11

Karin Labarai Masu Alaka

An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India Najeriya
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
  • Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.