Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Published: December 19, 2025 at 5:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 19, 2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu a ranar Alhamis ya ƙara jaddada ƙudurin sa na kafa ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa ya ba wa Amurka da abokan hulɗan Turai tabbacin cewa zai aiwatar da tsarin ’yan sandan jihohi a Najeriya.

Ya jaddada cewa dole ne a kafa ’yan sandan jihohi “ba tare da ja da baya ba” a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsaron cikin gida da ƙarfafa tsarin mulki a matakin jihohi.

Tinubu ya faɗi hakan ne a taron ƙungiyar manyan jiga-jigan APC karo na 14 da aka gudanar a Cibiyar Taron Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

A wajen taron, ya kuma dage cewa ’dole ne aiwatar da hukuncin cin gashin kan Kananan hukumomi a aikace, inda ya buƙaci gwamnonin jihohi da su daina riƙe kuɗaɗen da aka ware wa shugabannin ƙananan hukumomi.

Jawaban Shugaban Ƙasa sun zo ne a daidai lokacin da matsalolin tsaro ke ƙaruwa a faɗin ƙasar, tare da sabbin kiraye-kirayen neman kafa’yan sandan Jihohi, da kuma ƙoƙarin aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi da kuma raba musu kuɗi kai tsaye.

Tinubu ya shawarci shugabannin jam’iyya cewa APC, a matsayin ta na jam’iyya mai rinjaye, dole ne ta nuna jagoranci ta hanyar sasantawa, fahimtar juna da sassauci a matakin ƙasa, yana kuma ƙarfafa gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin abin da ke faruwa a jihohin su da ƙananan hukumomin su.

Ya ce kwanan nan ya tattauna da abokan hulɗa na ƙasashen waje, inda ya tabbatar musu da cewa Najeriya za ta tunkari tsarin ’yan sandan jihohi, yana mai ƙarawa da cewa yana da tabbacin jam’iyyar APC za ta bayar da cikakken goyon baya.

Yakara da cewa,“Na yi doguwar tattaunawa da su abokan hulɗa daga Amurka da Tura kuma na faɗa musu cikin alfahari cewa tabbas za mu zantas da dokar ’yan sandan jihohi domin inganta tsaro.”

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya
Next Post: Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu

Karin Labarai Masu Alaka

Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
  • Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
  • Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.