Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Published: December 19, 2025 at 5:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 19, 2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu a ranar Alhamis ya ƙara jaddada ƙudurin sa na kafa ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa ya ba wa Amurka da abokan hulɗan Turai tabbacin cewa zai aiwatar da tsarin ’yan sandan jihohi a Najeriya.

Ya jaddada cewa dole ne a kafa ’yan sandan jihohi “ba tare da ja da baya ba” a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsaron cikin gida da ƙarfafa tsarin mulki a matakin jihohi.

Tinubu ya faɗi hakan ne a taron ƙungiyar manyan jiga-jigan APC karo na 14 da aka gudanar a Cibiyar Taron Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

A wajen taron, ya kuma dage cewa ’dole ne aiwatar da hukuncin cin gashin kan Kananan hukumomi a aikace, inda ya buƙaci gwamnonin jihohi da su daina riƙe kuɗaɗen da aka ware wa shugabannin ƙananan hukumomi.

Jawaban Shugaban Ƙasa sun zo ne a daidai lokacin da matsalolin tsaro ke ƙaruwa a faɗin ƙasar, tare da sabbin kiraye-kirayen neman kafa’yan sandan Jihohi, da kuma ƙoƙarin aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi da kuma raba musu kuɗi kai tsaye.

Tinubu ya shawarci shugabannin jam’iyya cewa APC, a matsayin ta na jam’iyya mai rinjaye, dole ne ta nuna jagoranci ta hanyar sasantawa, fahimtar juna da sassauci a matakin ƙasa, yana kuma ƙarfafa gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin abin da ke faruwa a jihohin su da ƙananan hukumomin su.

Ya ce kwanan nan ya tattauna da abokan hulɗa na ƙasashen waje, inda ya tabbatar musu da cewa Najeriya za ta tunkari tsarin ’yan sandan jihohi, yana mai ƙarawa da cewa yana da tabbacin jam’iyyar APC za ta bayar da cikakken goyon baya.

Yakara da cewa,“Na yi doguwar tattaunawa da su abokan hulɗa daga Amurka da Tura kuma na faɗa musu cikin alfahari cewa tabbas za mu zantas da dokar ’yan sandan jihohi domin inganta tsaro.”

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya
Next Post: Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.