Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika

Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu
Published: December 19, 2025 at 11:21 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Rahotanni daga Jihar Nejan Najeriya na nuna cewa wata mace daga cikin mutane 17 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ta tutu a hannun ‘yanfashin dajin.

Tun a ranar 1/8/2025 ‘yanbindigar suka kutsa garin Ibeto a karamar Hukumar Magama suka kwashe mutane goma sha bakwai 14 daga cikin su matane sai kuma maza uku.

Masu garkuwar bukaci kudin fansa na naira milyan 150 kafin su sako wadan nan mutane, kuma har ya zuwa wannan lokaci mutanen garin na Ibeto basu hada wadannan kudaden ba.

Muhammad Kabir mazaunin garin na Ibeto yace tabbas sun samu labarin mutuwar daya daga cikin matan, sannan kuma wata matar guda da aka wuce da ita da ciki ta haihu a ranar Laraban nan da ta gabata.

Har yau dai babu wani bayani mai karfi daga bangaren gwamnatin Jihar Nejan akan kokarin karbo wadannan mutane na garin Ibeto,

Sai dai Shugaban karamar Hukumar ta Magama Dr. Muhmud Muhammad yace matsalar tana damunsu kuma cikin ikon Allah zasu samu mafita.

Kwamishinan Ma’aikatar kula da manyan Makarantun Jihar Nejan Farfesa Yakubu Auna, yace amatsayin su na masu ruwa da tsaki a yankin suna kokarin ganin an samu nasarar karbo wadannan mutane.

Mutuwar wannan baiwa Allah ta Ibeto a hannun ‘yanbindigar dai yana wuwa ne a dai dai lokacin da Kwamishina a hukumar Zabe ta jihar Neja Barista Ahmed Muhammad Borgu da Kuma tsohon shugaban Hukumar bada Ilimi bai daya ta jihar Nejan Hon. Alhasan Bawa Niworu suka share kimanin watanni uku a hannun ‘yanfashin da a yanzu haka bayanai ke nuna masu garkuwar sun bukaci milyan 300 kafin su sako su.

A yanzu dai hukumomin Jihar Nejan sun maida hankali wajan kokarin kubutar da sauran yara kimanin 200 da akayi garkuwa dasu a makarantar St Mary mallakar Cocin Katolica dake garin Papiri duk a Jihar Nejan.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/WATA-MATA-TA-MUTU-A-HANNUN-YANBINDIGA.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Next Post: Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.