Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu
Published: December 19, 2025 at 11:21 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Rahotanni daga Jihar Nejan Najeriya na nuna cewa wata mace daga cikin mutane 17 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ta tutu a hannun ‘yanfashin dajin.

Tun a ranar 1/8/2025 ‘yanbindigar suka kutsa garin Ibeto a karamar Hukumar Magama suka kwashe mutane goma sha bakwai 14 daga cikin su matane sai kuma maza uku.

Masu garkuwar bukaci kudin fansa na naira milyan 150 kafin su sako wadan nan mutane, kuma har ya zuwa wannan lokaci mutanen garin na Ibeto basu hada wadannan kudaden ba.

Muhammad Kabir mazaunin garin na Ibeto yace tabbas sun samu labarin mutuwar daya daga cikin matan, sannan kuma wata matar guda da aka wuce da ita da ciki ta haihu a ranar Laraban nan da ta gabata.

Har yau dai babu wani bayani mai karfi daga bangaren gwamnatin Jihar Nejan akan kokarin karbo wadannan mutane na garin Ibeto,

Sai dai Shugaban karamar Hukumar ta Magama Dr. Muhmud Muhammad yace matsalar tana damunsu kuma cikin ikon Allah zasu samu mafita.

Kwamishinan Ma’aikatar kula da manyan Makarantun Jihar Nejan Farfesa Yakubu Auna, yace amatsayin su na masu ruwa da tsaki a yankin suna kokarin ganin an samu nasarar karbo wadannan mutane.

Mutuwar wannan baiwa Allah ta Ibeto a hannun ‘yanbindigar dai yana wuwa ne a dai dai lokacin da Kwamishina a hukumar Zabe ta jihar Neja Barista Ahmed Muhammad Borgu da Kuma tsohon shugaban Hukumar bada Ilimi bai daya ta jihar Nejan Hon. Alhasan Bawa Niworu suka share kimanin watanni uku a hannun ‘yanfashin da a yanzu haka bayanai ke nuna masu garkuwar sun bukaci milyan 300 kafin su sako su.

A yanzu dai hukumomin Jihar Nejan sun maida hankali wajan kokarin kubutar da sauran yara kimanin 200 da akayi garkuwa dasu a makarantar St Mary mallakar Cocin Katolica dake garin Papiri duk a Jihar Nejan.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/WATA-MATA-TA-MUTU-A-HANNUN-YANBINDIGA.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Next Post: Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.