Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa
Published: November 20, 2025 at 3:25 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 20, 2025

Kungiyar Kwallon Kafa ta Enyimba dake ABA a Najeriya ta fidda wata takarda wacce ta raba wa manema labarai. Takardar dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar SAMPSON ORJI.

Inda suke nisanta kansu da wani labari da ya ja hankali a shafin sada zumuntar zamani cewar ƙungiyar ta Enyimba FC. Ta rage Albashin ‘Yan Wasa da kashi 50% bayan shan kaye a gida a hannun Wikki Tourist FC. daci 1-0 cikin gasar firimiya lig na Najeriya mako na 13.

Kungiyar Enyimba FC tace babu wani lokaci da shugabanninta suka amince, suka fara, ko aiwatar da wani rage albashi, na yan wasanta ba.

“Wannan rahoton wani abu ne kawai na tunanin marubucin kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi.” inji Enyimba.

Kungiyar ta nuna damuwa cewa irin wannan labarin karya ya fito ne daga wata kafar yada labarai da ake kyautata zaton ba tare da wani yunkurin tabbatar da sahihanci daga kungiyar ko ta hanyar shugabanninta ko kafofin watsa labaranta ba.

Kungiyar Enyimba FC, na goyon bayan girmama juna da kafofin watsa labarai da suka dade suna yi, ta ci gaba da mayar da hankali kan komawa ga hanyoyin nasara.

“Za mu ci gaba da yin aiki kafada da kafada da abokan hulɗar kafofin watsa labarai, don haskaka ayyukanmu da kuma ba da gudummawa ga ci gaban NPFL da ci gaban ƙwallon ƙafa a Najeriya.”

Hukumar shirya gasar cin kofin (NNL) a Najeriya ta tabbatar da janyewar ƙungiyar kwallon kafa ta Dakkada FC da ke Uyo daga gasar NNL26 mai zuwa.

“Hukumar ta yi alƙawarin daidaita jadawalin wasannin domin samar da hanyoyin da za a bi wajen cimma burin da aka sa a gaba. Hakan ya zama dole saboda janyewar ƙungiyar DAKKADA FC daga gasar.” Inji Hukumar.

DAGA KASAR GHANA:

Wani mamba a hukumar kula da wasan kwallon kafa ta kasar Ghana (GFA) Frederick Acheampong, ya ziyarci magoya bayan kulub din Aduana FC da suka ji rauni a wani hatsari a kan hanyarsu ta dawowa gida, bayan wasan GPL da su kayi da ƙungiyar kwallon kafar Asante Kotoko a Kumasi.

Hatsarin da ya jawo harda rasa rayuka. Frederick ya mika ta’aziyya ga iyalai da duk masoyan magoya bayan biyu da suka rasa rayukansu a hatsarin.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/RAHOTON-WASANNI-DARE-19-11-2025.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi Afrika
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.