Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata
Published: May 8, 2026 at 5:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 8, 2026

Gwamnatin jihar Kano a Najeriya ta kafa wani kwamitin mutum 12 domin dawo da naira biliyan 1.8 da aka ce an cire ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan gwamnati ta hannun kamfanonin bada lamuni masu zaman kansu.

Haka kuma gwamnatin ta dakatar da duk wata sabuwar yarjejeniyar rance tsakanin ma’aikatan gwamnati da kamfanonin lamunin, tana mai cewa daga yanzu ba za ta ƙara shiga tsakani a irin waɗannan yarjejeniyoyi ba.

Sakataren Gwamnatin Jiha, Umar Faruq Ibrahim, ya bayyana cewa wani bincike mai zaman kansa ya gano yadda wasu kamfanonin bada lamuni ke cire kuɗi daga albashin ma’aikata fiye da yadda doka ta tanada.

A cewarsa, dokar ta amince ne kada a cire fiye da kaso ɗaya bisa uku na albashin ma’aikaci, amma binciken ya nuna an karya wannan ƙa’ida.

Ya ce Majalisar Zartarwar Jihar ta amince da rahoton binciken tare da bai wa kwamitin da Kwamishinan Kuɗi, Ismaila Aliyu Danmaraya, ke jagoranta umarnin gano duk ma’aikatan da lamarin ya shafa, ko suna raye ko sun rasu, domin mayar musu da kuɗaɗensu.

SSG ɗin ya kuma bayyana cewa binciken ya wanke tsohon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Abdullahi Musa, daga zargin hannu a badakalar.

Ya ƙara da cewa tun farko an yi kuskuren bayyana cewa kuɗin da suka ɓace sun kai naira biliyan 1.5, sai dai binciken ya tabbatar da cewa adadin ya kai naira biliyan 1.8.

Gwamnatin ta kuma nuna damuwa kan yadda ma’aikata ke ci gaba da karɓar lamuni daga kamfanoni masu zaman kansu, inda ta bayyana cewa jimillar bashin da ake bin ma’aikatan gwamnati a yanzu ya kai kusan naira biliyan 13.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato
Next Post: Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
  • Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.