Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata
Published: May 8, 2026 at 5:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 8, 2026

Gwamnatin jihar Kano a Najeriya ta kafa wani kwamitin mutum 12 domin dawo da naira biliyan 1.8 da aka ce an cire ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan gwamnati ta hannun kamfanonin bada lamuni masu zaman kansu.

Haka kuma gwamnatin ta dakatar da duk wata sabuwar yarjejeniyar rance tsakanin ma’aikatan gwamnati da kamfanonin lamunin, tana mai cewa daga yanzu ba za ta ƙara shiga tsakani a irin waɗannan yarjejeniyoyi ba.

Sakataren Gwamnatin Jiha, Umar Faruq Ibrahim, ya bayyana cewa wani bincike mai zaman kansa ya gano yadda wasu kamfanonin bada lamuni ke cire kuɗi daga albashin ma’aikata fiye da yadda doka ta tanada.

A cewarsa, dokar ta amince ne kada a cire fiye da kaso ɗaya bisa uku na albashin ma’aikaci, amma binciken ya nuna an karya wannan ƙa’ida.

Ya ce Majalisar Zartarwar Jihar ta amince da rahoton binciken tare da bai wa kwamitin da Kwamishinan Kuɗi, Ismaila Aliyu Danmaraya, ke jagoranta umarnin gano duk ma’aikatan da lamarin ya shafa, ko suna raye ko sun rasu, domin mayar musu da kuɗaɗensu.

SSG ɗin ya kuma bayyana cewa binciken ya wanke tsohon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Abdullahi Musa, daga zargin hannu a badakalar.

Ya ƙara da cewa tun farko an yi kuskuren bayyana cewa kuɗin da suka ɓace sun kai naira biliyan 1.5, sai dai binciken ya tabbatar da cewa adadin ya kai naira biliyan 1.8.

Gwamnatin ta kuma nuna damuwa kan yadda ma’aikata ke ci gaba da karɓar lamuni daga kamfanoni masu zaman kansu, inda ta bayyana cewa jimillar bashin da ake bin ma’aikatan gwamnati a yanzu ya kai kusan naira biliyan 13.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato
Next Post: Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.