Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya yi rashin mahaifiyarsa Hajiya Umma, wadda ta rasu a ranar Juma’a.
Iyalin marigayiyar ne suka sanar da rasuwar a ranar da abin ya faru. Sun bayyana cewa marigayiyar ta daɗe tana fama da matsalolin lafiya da suka shafi tsufa, kuma halin lafiyarta ya ƙara tsananta a ‘yan kwanakin nan.
Rahotanni sun nuna cewa rashin lafiyarta ya ƙaru ne bayan ta ji labarin cewa ana tsare da ɗanta, El-Rufai, a hannun hukumomin tsaron Najeriya.
Iyalin sun kuma bayyana cewa El-Rufai yana kulawa sosai da lafiyar mahaifiyarsa kafin rasuwarta.


