Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya
Published: March 28, 2026 at 7:05 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya

APC Ta Yi Babb

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/APC-CONVENTION-ENDED-IN-CONSENSUS.mp3

an Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gudanar da babban taro na kasa inda ta amince da mukaman dukkanin shugabannin jam’iyyar ba hamayya.

Taron dai wanda shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a Abuja , ya samu halartar dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar daga fadin Najeriya.

“Masu sukar cewa mu na neman maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya ba haka ba ne, don ni na yi amanna da gasa a tsarin dimokradiyya amma hakan bai haramtawa kowa yin hulda da abokan siyasa ko jam’iyyar da ta kwanta ma sa a rai ba” Inji shugaba Tinubu a jawabin da ya gabatar cikin salon jamawninsa na magana daya bayan daya sannu-sannu kwana nesa.

Shugaban wanda ya nuna akwai kwarin guiwar gyaruwar lamura na kuncin tattalin arziki da a ke fuskanta, ya bukaci a yi shiru na minti daya don karrama marigayi shugaba Buhari da wani minti daya don sauran wadanda su ka kirkiro APC amma kuma sun kwanta dama.

Nan take a ka rantsar da shugabannin jam’iyyar karkashin jagorancin Nantawe Yilwatda daga jihar Filato.

Sakataren kudi na jam’iyyar Ambasada Haruna Gimsau ya ce ba sabon abu ba ne daidaitawa wajen fidda shugabannin jam’iyya.

Ita ma mataimakiyar shugabar mata ta jam’iyyar Zainab Abubakar wacce ta sauko daga dandalin rantsarwa ta na annashuwa, ta ce hakan kwarin guiwa ne kan babban zabe na 2027.

Shugaba Tinubu ya kare gyara da a ka yi ga dokar zabe ta 2023, ya na mai caccakar ‘yan adawa da cewa ba daidai ba ne su yi korafin kan gyaran.

 

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu
Next Post: Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa

Karin Labarai Masu Alaka

An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.