Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya
Published: March 28, 2026 at 7:05 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya

APC Ta Yi Babb

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/APC-CONVENTION-ENDED-IN-CONSENSUS.mp3

an Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gudanar da babban taro na kasa inda ta amince da mukaman dukkanin shugabannin jam’iyyar ba hamayya.

Taron dai wanda shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a Abuja , ya samu halartar dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar daga fadin Najeriya.

“Masu sukar cewa mu na neman maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya ba haka ba ne, don ni na yi amanna da gasa a tsarin dimokradiyya amma hakan bai haramtawa kowa yin hulda da abokan siyasa ko jam’iyyar da ta kwanta ma sa a rai ba” Inji shugaba Tinubu a jawabin da ya gabatar cikin salon jamawninsa na magana daya bayan daya sannu-sannu kwana nesa.

Shugaban wanda ya nuna akwai kwarin guiwar gyaruwar lamura na kuncin tattalin arziki da a ke fuskanta, ya bukaci a yi shiru na minti daya don karrama marigayi shugaba Buhari da wani minti daya don sauran wadanda su ka kirkiro APC amma kuma sun kwanta dama.

Nan take a ka rantsar da shugabannin jam’iyyar karkashin jagorancin Nantawe Yilwatda daga jihar Filato.

Sakataren kudi na jam’iyyar Ambasada Haruna Gimsau ya ce ba sabon abu ba ne daidaitawa wajen fidda shugabannin jam’iyya.

Ita ma mataimakiyar shugabar mata ta jam’iyyar Zainab Abubakar wacce ta sauko daga dandalin rantsarwa ta na annashuwa, ta ce hakan kwarin guiwa ne kan babban zabe na 2027.

Shugaba Tinubu ya kare gyara da a ka yi ga dokar zabe ta 2023, ya na mai caccakar ‘yan adawa da cewa ba daidai ba ne su yi korafin kan gyaran.

 

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu
Next Post: Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika
An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.