Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi
Published: January 23, 2026 at 9:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rikon sakainar kashi da iyaye da sauran masu ruwa da tsaki ke yi wa dokokin da suka kare hakkin yara, na daga dalilan da al’umma ke samun kanta cikin bala’o’i da rashin tabbas.

Dokokin da suka ba yara ‘yancin samun kariya daga duk wani yanayi da zai cutar da rayuwarsu ta kowace fuska, na shimfide a kundi na majalisar dinkin duniya da na nahiya da kasa da kuma jihohi.

A wani horo da majalisar dinkin duniya da hadin guiwan cibiyar dake da’awar Samar da dokoki wa al’umma, wato CISLAC da cibiyar dake kula da yara, wato SOS Children Village Nigeria, suka yi wa ‘yan jarida a Jos, an shafe kwanaki uku ana tattaunawa kan matakan kula da yara da dokokin da suka bada kariya wa yaran.

Wani lauya mai zaman kansa, Barista Dariyem Kruslat yace al’umma da hukumomi suna da gagarumin hakki na kula da yara tun daga haihuwarsu har lokacin da zasu ci gashin kansu, don daidaita rayuwarsu.

Malama Grace Solomon dake aiki a kungiyar dake kare yara, Child Protection Network tace yara ‘yan kasa da shekaru goma sha takwas ba zasu iya kare kansu ba, don haka ya wajaba manya su kare su.

Mr Solomon Adoga na cibiyar CISLAC yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawa wajen bada kariya wa yara a Najeriya.

Adoga ya kara da cewa aikin ‘yan jarida bai tsaya a iyayin rahoto kan batutuwa da suka jibanci ‘yan cin yara ko hanyoyin basu kariya kadai ba, har ma da tabbatar da duk wanda keda ruwa da tsaki wajen aiwatar da dokoki da tsare-tsaren hukumomi, sun gudanar da aikinsu.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260123-WA0085-1.mp3
Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke
Next Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida

Karin Labarai Masu Alaka

Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.