Rikon sakainar kashi da iyaye da sauran masu ruwa da tsaki ke yi wa dokokin da suka kare hakkin yara, na daga dalilan da al’umma ke samun kanta cikin bala’o’i da rashin tabbas.
Dokokin da suka ba yara ‘yancin samun kariya daga duk wani yanayi da zai cutar da rayuwarsu ta kowace fuska, na shimfide a kundi na majalisar dinkin duniya da na nahiya da kasa da kuma jihohi.
A wani horo da majalisar dinkin duniya da hadin guiwan cibiyar dake da’awar Samar da dokoki wa al’umma, wato CISLAC da cibiyar dake kula da yara, wato SOS Children Village Nigeria, suka yi wa ‘yan jarida a Jos, an shafe kwanaki uku ana tattaunawa kan matakan kula da yara da dokokin da suka bada kariya wa yaran.
Wani lauya mai zaman kansa, Barista Dariyem Kruslat yace al’umma da hukumomi suna da gagarumin hakki na kula da yara tun daga haihuwarsu har lokacin da zasu ci gashin kansu, don daidaita rayuwarsu.
Malama Grace Solomon dake aiki a kungiyar dake kare yara, Child Protection Network tace yara ‘yan kasa da shekaru goma sha takwas ba zasu iya kare kansu ba, don haka ya wajaba manya su kare su.
Mr Solomon Adoga na cibiyar CISLAC yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawa wajen bada kariya wa yara a Najeriya.
Adoga ya kara da cewa aikin ‘yan jarida bai tsaya a iyayin rahoto kan batutuwa da suka jibanci ‘yan cin yara ko hanyoyin basu kariya kadai ba, har ma da tabbatar da duk wanda keda ruwa da tsaki wajen aiwatar da dokoki da tsare-tsaren hukumomi, sun gudanar da aikinsu.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


