Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi
Published: January 23, 2026 at 9:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rikon sakainar kashi da iyaye da sauran masu ruwa da tsaki ke yi wa dokokin da suka kare hakkin yara, na daga dalilan da al’umma ke samun kanta cikin bala’o’i da rashin tabbas.

Dokokin da suka ba yara ‘yancin samun kariya daga duk wani yanayi da zai cutar da rayuwarsu ta kowace fuska, na shimfide a kundi na majalisar dinkin duniya da na nahiya da kasa da kuma jihohi.

A wani horo da majalisar dinkin duniya da hadin guiwan cibiyar dake da’awar Samar da dokoki wa al’umma, wato CISLAC da cibiyar dake kula da yara, wato SOS Children Village Nigeria, suka yi wa ‘yan jarida a Jos, an shafe kwanaki uku ana tattaunawa kan matakan kula da yara da dokokin da suka bada kariya wa yaran.

Wani lauya mai zaman kansa, Barista Dariyem Kruslat yace al’umma da hukumomi suna da gagarumin hakki na kula da yara tun daga haihuwarsu har lokacin da zasu ci gashin kansu, don daidaita rayuwarsu.

Malama Grace Solomon dake aiki a kungiyar dake kare yara, Child Protection Network tace yara ‘yan kasa da shekaru goma sha takwas ba zasu iya kare kansu ba, don haka ya wajaba manya su kare su.

Mr Solomon Adoga na cibiyar CISLAC yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawa wajen bada kariya wa yara a Najeriya.

Adoga ya kara da cewa aikin ‘yan jarida bai tsaya a iyayin rahoto kan batutuwa da suka jibanci ‘yan cin yara ko hanyoyin basu kariya kadai ba, har ma da tabbatar da duk wanda keda ruwa da tsaki wajen aiwatar da dokoki da tsare-tsaren hukumomi, sun gudanar da aikinsu.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260123-WA0085-1.mp3
Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke
Next Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.