Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi
Published: December 5, 2025 at 7:57 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Najeriya ta amince da biyan kudi Naira biliyan 185 ga kamfanonin samar albarkatun mai da suke bin ta bashi da irin gas da suke samarwa ga injunan samar da wutar lantarki a kasar, domin karfafa bangaren makamashi da inganta samar da wutar lantarki.

Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa dake karkashin jagorancin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, ita ce ta amince da biyan kudin bayan shugaba Bola Tinubu ya bayarda umurnin a biya wadannan basussukan dake neman gurgunta mai da gas da ake bukata ga masana’antun samar da wutar lantarki a kasar.

Karamin ministan man fetur Ekperikpe Ekpo, ya ce za a biya wadannan basussuka ne ta hanyar Zarmiya, wato kamfanonin zasu cire wadannan kudade daga kudaden da ya kamata su biya gwamnati na man da suke dauka daga kasar

Najeriya, kasar da ta fi kowacce yawan jama’a a nahiyar Afirka, tana ci gaba da fuskantar karancin wutar lantarki da aka kasa shawo kansa shekara da shekaru, abinda ke dakushe harkokin kasuwanci da na tattalin arzikin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Next Post: Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu Afrika
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.