Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram
Published: January 12, 2026 at 12:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Operation Hadin Kai (OPHK) sun ƙara zafafa hare-haren su kan mayakan Boko Haram da ISWAP a jihar Borno, wanda ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addanci.

A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da manema labarai na Rundunar Haɗin Gwiwa a Arewa Maso Gabas, Laftanal Kanar Sani Uba ya fitar, dakarun sun tilasta wa ‘yan ta’adda 11 su miƙa wuƙa a yankin Azir–Wajiroko tare da mayar da AK-47 da harsasai daban-daban.

A ranar 9 ga Janairu, 2026, dakarun sun gudanar da gagarumin farmaki a yankin Bula-galda, inda suka lalata sansanonin ‘yan ta’adda a Dagumba, Bonne, Yaganari, Gosuri da Umchile, kuma lokacin farmakin, an rusa mafaka da dama, an katse hanyoyin samar musu da kayan aiki, kuma an kwato tutocin ta’addanci, bindigogi da makamai.

A wasu farmakin da suka gudana a yankunan Yale da Bula Gaida, sojojin sun sake rusa cibiyoyin kayan aiki na ‘yan ta’adda, tare da kwato bindigogi, harsasai da bindigar gurneti.

Haka kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, dakarun sun fafata da mayaƙan JAS/ISWAP a tsakanin kauyukan Sojiri da Kayamla, inda suka kashe ‘yan ta’adda 8.
An kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin suna ba da kayan aiki ga ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Gubio.

Rundunar Sojojin Najeriya ta jaddada kudirinta na dawo da zaman lafiya a Arewa maso Gabas tare da roƙon al’umma da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimaka musu a yaki da ta’addanci.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup 
Next Post: Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma Afrika
Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
  • Zulum Ya Jinjinawa Hadiza Aliyu Kan Naɗin Ta A Matsayin Babbar Editar NAN Afrika
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.