Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram
Published: January 12, 2026 at 12:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Operation Hadin Kai (OPHK) sun ƙara zafafa hare-haren su kan mayakan Boko Haram da ISWAP a jihar Borno, wanda ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addanci.

A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da manema labarai na Rundunar Haɗin Gwiwa a Arewa Maso Gabas, Laftanal Kanar Sani Uba ya fitar, dakarun sun tilasta wa ‘yan ta’adda 11 su miƙa wuƙa a yankin Azir–Wajiroko tare da mayar da AK-47 da harsasai daban-daban.

A ranar 9 ga Janairu, 2026, dakarun sun gudanar da gagarumin farmaki a yankin Bula-galda, inda suka lalata sansanonin ‘yan ta’adda a Dagumba, Bonne, Yaganari, Gosuri da Umchile, kuma lokacin farmakin, an rusa mafaka da dama, an katse hanyoyin samar musu da kayan aiki, kuma an kwato tutocin ta’addanci, bindigogi da makamai.

A wasu farmakin da suka gudana a yankunan Yale da Bula Gaida, sojojin sun sake rusa cibiyoyin kayan aiki na ‘yan ta’adda, tare da kwato bindigogi, harsasai da bindigar gurneti.

Haka kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, dakarun sun fafata da mayaƙan JAS/ISWAP a tsakanin kauyukan Sojiri da Kayamla, inda suka kashe ‘yan ta’adda 8.
An kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin suna ba da kayan aiki ga ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Gubio.

Rundunar Sojojin Najeriya ta jaddada kudirinta na dawo da zaman lafiya a Arewa maso Gabas tare da roƙon al’umma da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimaka musu a yaki da ta’addanci.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup 
Next Post: Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya

Karin Labarai Masu Alaka

Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.