Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma
Published: July 13, 2026 at 6:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce ci gaba da tattaunawa da kuma daukar matakin gaggawa kan matsalolin da ke tasowa shi ne mafita wajen hana rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar.

CP Chuso ya bayyana haka ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan rikicin makiyaya da manoma da aka gudanar a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe.

Ya ce idan shugabannin al’umma a matakai daban-daban suka rika magance matsalolin tun kafin su rikide zuwa rikici, za a samu raguwar rikice-rikicen makiyaya da manoma.

Kwamishinan ‘yan sandan ya bayyana cewa dalilan rikicin makiyaya da manoma sun bambanta daga wannan yanki zuwa wani, don haka akwai bukatar duk masu ruwa da tsaki su hada kai wajen samar da mafita mai dorewa.


Ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa kafa kwamitocin sasanta rikice-rikice a matakai daban-daban, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen rage nauyin da ke kan rundunar ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

Taron ya tattauna kan muhimman batutuwa da suka hada da mamaye hanyoyin shanun kiwo, samar da wuraren kiwo na zamani (ranches), zirga-zirgar dabbobi daga jiha zuwa jiha domin kiwo, da kuma hanyoyin gaggauta kai rahoton duk wata matsala domin daukar matakin da ya dace cikin lokaci.


Taron ya samu halartar sarakunan gargajiya, shugabannin addinai, shugabannin makiyaya na Fulani da suka Gudanar da jawabai amadadin mabiyansu Daga dukkan Sassan jihar Gombe da kuma manyan jami’an rundunar ‘yan sanda daga kananan hukumomi goma sha daya na jihar Gombe, domin karfafa hadin gwiwa wajen tabbatar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi
Next Post: An Bude Gasar Bauchi Annual International Polo 2026

Karin Labarai Masu Alaka

PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci Labarai
An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.