Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar da sake zaɓar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027 ƙarƙashin jam’iyyar APC.
Wannan mataki ya kawo ƙarshen jita-jitar da ta dade tana yawo kan yiwuwar sauya mataimakin shugaban ƙasar gabanin zaɓen mai zuwa.
Tinubu da Shettima ne suka yi nasarar lashe zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023, kuma yanzu za su sake neman wa’adin mulki na biyu a zaɓen 2027 idan suka samu amincewar jam’iyyar da kuma cika dukkan sharuɗɗan zaɓe.


