Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa
Published: March 31, 2026 at 6:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyoyin mata a jihar Filato sun bi sahin takwarorinsu a fadin Najeriya wajen yin gangami don kara karfafa bukatar su na neman kujeru saba’in da hudu a majalisar wakilan Najeriya.

Kujeru na musamman wa mata a majalisar wakilan Najeriya, wanda aka fi sani da HB1349, mataimakin kakakin majalisar wakilan Najeriya, Honarabul Benjamin Okezie da wassu ‘yan majalisar su goma sha biyu ne suka gabatar sa kudirin.

Kudirin yana neman sauya kundin tsarin mulki na alibi dari tara da tasa’in da tara ne don samar da karin kujeru wa mata, don magance karancin wakilcin mata a majalisun dokoki, da yanzu yake kasa da kashi biyar.

Honarabul Esther Dusu, tsohuwar ‘yar majalisa ce a majalisar dokokin jihar Filato wacce kuma ta jagoranci gangamin, tace abinda suke bukata shine samun gurabe da zasu taimaka wa mata.

Madam Selina Ali, shugaban kungiyar majalisar kungiyoyin mata a Najeriya, NCWS, reshen jihar Filato tace rashin mata a majalisu ya sanya ba’a jin muryoyinsu da bukatunsu.

Shugaban kungiyar mata musulmi ta FOMWAN, reshen jihar Filato, Hauwa Umar Musa tace guraben da aka ba mata, har yanzu basu wadatar ba.

Itama Madam Sarah Dalut, Shugaban kungiyar matan Kirista a jihar Filato, tace ba fada suke yi da maza ba, suna dai bukatar samun karin kaso ne.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata a Jihar Filato, Grace Akwe Gotip ta karfafa aniyar bada gudunmowar ganin mata sun furta matsalolin su don samun gyara.

A defender guda kuwa, mamba mai wakiltar Jos ta Arewan Arewa a majalisar dokokin jihar Filato, Adamu Aliyu yace suna kan kokarin samarda dokokin da zasu ba mata ‘yanci.

Bayanai na nuni da cewa mata a Najeriya na da kujeeru ishirin da daya ne kachal daga cikin kujeru dari hudu da sittin da tara a majalisun dokokin kasar, a kididdiga ta karshen shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar.

Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260331-WA0012.mp3

 

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
Next Post: Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass Afrika
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
‘Yan Sandan Gombe Sun Yi Taron Gaggawa Da Jam’iyyun Siyasa Da INEC Kan Tsaro Labarai
Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
  • Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa Afrika
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027 Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.