Kungiyoyin mata a jihar Filato sun bi sahin takwarorinsu a fadin Najeriya wajen yin gangami don kara karfafa bukatar su na neman kujeru saba’in da hudu a majalisar wakilan Najeriya.
Kujeru na musamman wa mata a majalisar wakilan Najeriya, wanda aka fi sani da HB1349, mataimakin kakakin majalisar wakilan Najeriya, Honarabul Benjamin Okezie da wassu ‘yan majalisar su goma sha biyu ne suka gabatar sa kudirin.
Kudirin yana neman sauya kundin tsarin mulki na alibi dari tara da tasa’in da tara ne don samar da karin kujeru wa mata, don magance karancin wakilcin mata a majalisun dokoki, da yanzu yake kasa da kashi biyar.
Honarabul Esther Dusu, tsohuwar ‘yar majalisa ce a majalisar dokokin jihar Filato wacce kuma ta jagoranci gangamin, tace abinda suke bukata shine samun gurabe da zasu taimaka wa mata.
Madam Selina Ali, shugaban kungiyar majalisar kungiyoyin mata a Najeriya, NCWS, reshen jihar Filato tace rashin mata a majalisu ya sanya ba’a jin muryoyinsu da bukatunsu.
Shugaban kungiyar mata musulmi ta FOMWAN, reshen jihar Filato, Hauwa Umar Musa tace guraben da aka ba mata, har yanzu basu wadatar ba.
Itama Madam Sarah Dalut, Shugaban kungiyar matan Kirista a jihar Filato, tace ba fada suke yi da maza ba, suna dai bukatar samun karin kaso ne.
Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata a Jihar Filato, Grace Akwe Gotip ta karfafa aniyar bada gudunmowar ganin mata sun furta matsalolin su don samun gyara.
A defender guda kuwa, mamba mai wakiltar Jos ta Arewan Arewa a majalisar dokokin jihar Filato, Adamu Aliyu yace suna kan kokarin samarda dokokin da zasu ba mata ‘yanci.
Bayanai na nuni da cewa mata a Najeriya na da kujeeru ishirin da daya ne kachal daga cikin kujeru dari hudu da sittin da tara a majalisun dokokin kasar, a kididdiga ta karshen shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar.
Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


