Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa
Published: March 31, 2026 at 6:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyoyin mata a jihar Filato sun bi sahin takwarorinsu a fadin Najeriya wajen yin gangami don kara karfafa bukatar su na neman kujeru saba’in da hudu a majalisar wakilan Najeriya.

Kujeru na musamman wa mata a majalisar wakilan Najeriya, wanda aka fi sani da HB1349, mataimakin kakakin majalisar wakilan Najeriya, Honarabul Benjamin Okezie da wassu ‘yan majalisar su goma sha biyu ne suka gabatar sa kudirin.

Kudirin yana neman sauya kundin tsarin mulki na alibi dari tara da tasa’in da tara ne don samar da karin kujeru wa mata, don magance karancin wakilcin mata a majalisun dokoki, da yanzu yake kasa da kashi biyar.

Honarabul Esther Dusu, tsohuwar ‘yar majalisa ce a majalisar dokokin jihar Filato wacce kuma ta jagoranci gangamin, tace abinda suke bukata shine samun gurabe da zasu taimaka wa mata.

Madam Selina Ali, shugaban kungiyar majalisar kungiyoyin mata a Najeriya, NCWS, reshen jihar Filato tace rashin mata a majalisu ya sanya ba’a jin muryoyinsu da bukatunsu.

Shugaban kungiyar mata musulmi ta FOMWAN, reshen jihar Filato, Hauwa Umar Musa tace guraben da aka ba mata, har yanzu basu wadatar ba.

Itama Madam Sarah Dalut, Shugaban kungiyar matan Kirista a jihar Filato, tace ba fada suke yi da maza ba, suna dai bukatar samun karin kaso ne.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata a Jihar Filato, Grace Akwe Gotip ta karfafa aniyar bada gudunmowar ganin mata sun furta matsalolin su don samun gyara.

A defender guda kuwa, mamba mai wakiltar Jos ta Arewan Arewa a majalisar dokokin jihar Filato, Adamu Aliyu yace suna kan kokarin samarda dokokin da zasu ba mata ‘yanci.

Bayanai na nuni da cewa mata a Najeriya na da kujeeru ishirin da daya ne kachal daga cikin kujeru dari hudu da sittin da tara a majalisun dokokin kasar, a kididdiga ta karshen shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar.

Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260331-WA0012.mp3

 

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
Next Post: Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
  • Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.