Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa
Published: March 31, 2026 at 6:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyoyin mata a jihar Filato sun bi sahin takwarorinsu a fadin Najeriya wajen yin gangami don kara karfafa bukatar su na neman kujeru saba’in da hudu a majalisar wakilan Najeriya.

Kujeru na musamman wa mata a majalisar wakilan Najeriya, wanda aka fi sani da HB1349, mataimakin kakakin majalisar wakilan Najeriya, Honarabul Benjamin Okezie da wassu ‘yan majalisar su goma sha biyu ne suka gabatar sa kudirin.

Kudirin yana neman sauya kundin tsarin mulki na alibi dari tara da tasa’in da tara ne don samar da karin kujeru wa mata, don magance karancin wakilcin mata a majalisun dokoki, da yanzu yake kasa da kashi biyar.

Honarabul Esther Dusu, tsohuwar ‘yar majalisa ce a majalisar dokokin jihar Filato wacce kuma ta jagoranci gangamin, tace abinda suke bukata shine samun gurabe da zasu taimaka wa mata.

Madam Selina Ali, shugaban kungiyar majalisar kungiyoyin mata a Najeriya, NCWS, reshen jihar Filato tace rashin mata a majalisu ya sanya ba’a jin muryoyinsu da bukatunsu.

Shugaban kungiyar mata musulmi ta FOMWAN, reshen jihar Filato, Hauwa Umar Musa tace guraben da aka ba mata, har yanzu basu wadatar ba.

Itama Madam Sarah Dalut, Shugaban kungiyar matan Kirista a jihar Filato, tace ba fada suke yi da maza ba, suna dai bukatar samun karin kaso ne.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata a Jihar Filato, Grace Akwe Gotip ta karfafa aniyar bada gudunmowar ganin mata sun furta matsalolin su don samun gyara.

A defender guda kuwa, mamba mai wakiltar Jos ta Arewan Arewa a majalisar dokokin jihar Filato, Adamu Aliyu yace suna kan kokarin samarda dokokin da zasu ba mata ‘yanci.

Bayanai na nuni da cewa mata a Najeriya na da kujeeru ishirin da daya ne kachal daga cikin kujeru dari hudu da sittin da tara a majalisun dokokin kasar, a kididdiga ta karshen shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar.

Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260331-WA0012.mp3

 

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
Next Post: Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
  • Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.