Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
Published: March 31, 2026 at 6:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 31, 2026

Gwamnatin jihar Filato ta ayyana dokar hana fita na kwanaki biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Matakin ya biyo bayan wani harin kan-mai-uwa-da-wabi da ‘yan bindiga suka kai a Unguwar Rukuba dake cikin birnin Jos.

Harin da ‘yan bindigar suka kawo da misalin karfe takwas na daren Lahadi, bayanai daga shaidun gani da ido na nuni da cewa, ‘yan bindigar sun zo ne a kan babura da mota kirar sharon, wanda yayi kama da na jami’an dake yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da fuskokinsu a rufe, suka bude wuta a wata mahada da ta kasance kamar kasuwa, ake hada-hada dare da rana.

A sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa na jihar, Madam Joyce Ramnap, matakin sanya dokar hana zirga-zirgar ya zama dole, don samadda damar shapke wadanda suka yi barnar don hukunta su.

Matakin shugaban karamar hukumar Jos ta Arewa, Muhammad Kabiru Garkuwa, yace an dade ba’a ga irin wannan mummunan lamari a cikin garin Jos ba, don haka hukumomi na yin duk mai yiwuwa wajen hana maida hannun agogo baya a lamarin tsaro.

Duk da shike hukumomi basu bada adadin wadanda suka rasa rayukansu a harin ba, wata mace da bata amince in bayyana ta ba, ta shaida min cewa ta ga gawarwaki talatin da uku.

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya kai ziyarar jaje a Unguwar Rukuba, inda ya ba matasa hakurin kada su dauki doka a hannunsu, don kaucewa kashe wadanda basu ji ba basu gani ba.

 

Daga Jos Ga Rahoton Zainab Babaji

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260331-WA0007.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu
Next Post: Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsofin Ma’aikatan Gwamnati Sunyi Zanga Zanga A Jihar Neja Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
  • An Tsaurara Tsaro Yayin Da Tehran Ke Shirin Karɓar Masu Jimamin Ayatollah Khamenei Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
  • Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.