Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
Published: March 31, 2026 at 6:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 31, 2026

Gwamnatin jihar Filato ta ayyana dokar hana fita na kwanaki biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Matakin ya biyo bayan wani harin kan-mai-uwa-da-wabi da ‘yan bindiga suka kai a Unguwar Rukuba dake cikin birnin Jos.

Harin da ‘yan bindigar suka kawo da misalin karfe takwas na daren Lahadi, bayanai daga shaidun gani da ido na nuni da cewa, ‘yan bindigar sun zo ne a kan babura da mota kirar sharon, wanda yayi kama da na jami’an dake yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da fuskokinsu a rufe, suka bude wuta a wata mahada da ta kasance kamar kasuwa, ake hada-hada dare da rana.

A sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa na jihar, Madam Joyce Ramnap, matakin sanya dokar hana zirga-zirgar ya zama dole, don samadda damar shapke wadanda suka yi barnar don hukunta su.

Matakin shugaban karamar hukumar Jos ta Arewa, Muhammad Kabiru Garkuwa, yace an dade ba’a ga irin wannan mummunan lamari a cikin garin Jos ba, don haka hukumomi na yin duk mai yiwuwa wajen hana maida hannun agogo baya a lamarin tsaro.

Duk da shike hukumomi basu bada adadin wadanda suka rasa rayukansu a harin ba, wata mace da bata amince in bayyana ta ba, ta shaida min cewa ta ga gawarwaki talatin da uku.

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya kai ziyarar jaje a Unguwar Rukuba, inda ya ba matasa hakurin kada su dauki doka a hannunsu, don kaucewa kashe wadanda basu ji ba basu gani ba.

 

Daga Jos Ga Rahoton Zainab Babaji

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260331-WA0007.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu
Next Post: Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika
An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.