‘Yan bindiga sun hallaka fiye da mutane 70 a Sudan ta Kudu biyo bayan rikici kan hakar gwal a gefen Juba, babban birnin kasar a karshen makon da ya gabata a cewar ‘yan sanda ranar Litinin.
Wani hoton video da aka yada a yanar gizo ya nuna gawawwakin mutane zube a kasa. Wani dan jarida a wajen yace akwai mutanen da abun ya shafa da yawa da ake tsammanin sun tsere cikin daji.
Cibiyar hakar gwal ta Jebel Iraq dake jihar Central Equatoria, a baya ta sha fama rigingimu da suka hada da masu hakar gwal da doka bata basu izini ba. A sudan ta Kudu, yawanci ba’a kafawa hakar gwal ka’ida, inda gwamnatocin jihohi suke tafiyar da nasu bangarorin da ban da na gwamnatin tarayya.
Mai magana da yawun ‘yan sanda Kwacijwok Dominic Amondoc, yace zai yi karin sharhi kan harin idan ya samu karin bayani. Yace a yanzu abinda ya sani kawai shine wasu ‘yan bindiga da ba’a san ko su wanene ba sun kai hari wurin hakar gwal dake Jebel Iraq. Mutane fiye da 70 sun hallaka, da yawa kuma sun samu raunuka.


