Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ranar Lahadi ya jadda cewar Amincewa da ‘yancin Iran na inganta makamashin Uranium na da muhimmanci ga tattaunawar nukiliya da Amurka don samun nasara.
Jami’an diflomasiyyar Amurka da na Iran sun gudanar da tattaunawa kai tsaye a kasar Oman tun a ranar Juma’a, da nufin farfado da harkokin diflomasiyya a daidai lokacin da sojojin ruwan Amurka ke ci gaba da mamaye bakin ruwan Iran, duk kuwa da irin alƙawarin mayar da martani mai zafi idan aka kai musu hari a cewar Iran.
Arakchi ya ce, “Ba za mu taba amincewa da wata barazana ba. Don haka, muna bukatar mu mai da hankali kan tattaunawar da za ta samu karbuwa a cikin Iran tare da karfafawa Iran daukar duk wasu matakai na kare kanta.


