Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total
Published: February 9, 2026 at 2:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a kasar Namibiya sun ce ba za su amince da yarjejeniyar siyan hannun jari da kamfanin TotalEnergies yayi ba, biyo bayan wata sanarwa da ta fitar a makon da ya gabata, ranar lahadi hukumomin sun ce duk wani kamfani da ke son yin mu’amala to sai ya bi duk ka’idoji da aka shardanta.

Jonas Mbambo, mai magana da yawun fadar shugaban kasar, ya tabbatar da cewa har sai an gabatar da takarda a hukumance sannan kuma an kammala tsarin da aka tsara, ya kuma kara da cewar “babu wani ciniki da za a iya ganewa ko a ce yana da inganci”.

Babban kamfanin mai na Faransa TotalEnergies da Petrobras na Brazil sun ce a ranar Juma’a kowannensu ya samu kaso 42.5% na lasisin hakar mai na PEL104 a gabar tekun Namibiya, yayin da kamfanonin biyu ke kokarin hako mai a daya daga cikin iyakokin duniya na karshe.

Saye daga hannun kamfanin Maravilla Oil and Gas da kamfanin Eight Offshore Investments Holdings, ya nuna fadada hannun jarin kamfanin na Total a kasar dake kudancin Afirka, inda take fatan zaman farko da zata samar da mai nan da karshen shekaru goma.

Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha
Next Post: Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba Labarai
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi Amurka
  • Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.