Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe
Published: February 1, 2026 at 1:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 1, 2026

An Kaddamar da Kwamitin Gasar Kofin Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na Gombe 2026

An kaddamar da Kwamitin Shirya Gasar Ƙwallon Ƙafa ta Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na jihar Gombe dake arewa maso gabashin Najeriya, wadda aka fi sani da Kofin Haɗin Kan Sarkin Gombe 2026, a hukumance a birnin Gombe.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a taron farko na kwamitin, inda aka miƙa wa mambobinsa takardun shaidar aikinsu. Bayan haka, an gudanar da taron manema labarai da ya samu halartar wakilan manyan kafafen yaɗa labarai.

Da yake jawabi yayin taron, Shugaban Kwamitin kuma mai ɗaukar nauyin gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya bayyana cewa an shirya gasar ne domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya da kuma bunƙasa matasa ta hanyar wasanni a masarautun gargajiya na jihar.

Ya ƙara da cewa gasar za ta gudana ne da tsarin haɗaka, inda za a raba ƙungiyoyin da za su fafata gida huɗu a cibiyoyi huɗu, bisa shawarwarin da Kwamitin Fasaha zai bayar.

Ahmed Shuaibu Gara Gombe ya kuma sanar da kyaututtuka masu tsoka da aka tanada kuma kungiyar da ta zama zakara za ta samu naira miliyan biyar tare da kofi, ta biyu kuma naira miliyan uku, yayin da ta uku za ta samu naira miliyan biyu.

Haka kuma za a bayar da lambobin yabo na musamman ga Mafi Kyawun Mai Tsaron Raga, Wanda Ya Fi Zura Ƙwallaye, Fitaccen Ɗan Wasa na Gasar, da kuma Ƙungiyar da Ta Fi Nuna Wasan Gaskiya, duk tare da kofuna.

Mai ɗaukar nauyin gasar ya kuma bayyana cewa za a fara rangadin nuna kofin gasar a faɗin jihar daga Litinin, 2 ga Fabrairu, 2026, zuwa Jumma’a, 6 ga Fabrairu, 2026.

Rangadin zai zagaya dukkan masarautun gargajiya 15 na jihar, farawa daga Masarautun Nafada da Funakaye, sannan ya wuce Yamaltu, Deba, Waja, Kaltungo, Tangale, Akko, Pindiga, Cham, Dadiya, Tula, Gona, da Dukku.

Ana shirya gasar Kofin Sarkin Gombe ta 2026 ne tare da ɗaukar nauyinta daga kamfanin Green White Green Sports Center Limited, tare da goyon bayan Mai Martaba Sarkin Gombe.

Ana sa ran gasar za ta ƙara bunƙasa harkokin ƙwallon ƙafa a matakin tushe tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin al’ummomin jihar Gombe.

Kwamitin shirya gasar na ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe a matsayin Shugaba, yayin da Auwal Musa Umar, tsohon Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta jihar Gombe, ke matsayin Mataimakin Shugaba.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya da wakilan al’umma, yayin da Haruna Abdullahi yake a matsayin Sakatare da Yakubu Maikudi Jami’an yada labarai tare da masu kula da harkokin yaɗa labarai da tallafin tsare-tsare na Musamman.

Labarai, Najeriya, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga
Next Post: Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
  • An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.