Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe
Published: February 1, 2026 at 1:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 1, 2026

An Kaddamar da Kwamitin Gasar Kofin Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na Gombe 2026

An kaddamar da Kwamitin Shirya Gasar Ƙwallon Ƙafa ta Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na jihar Gombe dake arewa maso gabashin Najeriya, wadda aka fi sani da Kofin Haɗin Kan Sarkin Gombe 2026, a hukumance a birnin Gombe.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a taron farko na kwamitin, inda aka miƙa wa mambobinsa takardun shaidar aikinsu. Bayan haka, an gudanar da taron manema labarai da ya samu halartar wakilan manyan kafafen yaɗa labarai.

Da yake jawabi yayin taron, Shugaban Kwamitin kuma mai ɗaukar nauyin gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya bayyana cewa an shirya gasar ne domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya da kuma bunƙasa matasa ta hanyar wasanni a masarautun gargajiya na jihar.

Ya ƙara da cewa gasar za ta gudana ne da tsarin haɗaka, inda za a raba ƙungiyoyin da za su fafata gida huɗu a cibiyoyi huɗu, bisa shawarwarin da Kwamitin Fasaha zai bayar.

Ahmed Shuaibu Gara Gombe ya kuma sanar da kyaututtuka masu tsoka da aka tanada kuma kungiyar da ta zama zakara za ta samu naira miliyan biyar tare da kofi, ta biyu kuma naira miliyan uku, yayin da ta uku za ta samu naira miliyan biyu.

Haka kuma za a bayar da lambobin yabo na musamman ga Mafi Kyawun Mai Tsaron Raga, Wanda Ya Fi Zura Ƙwallaye, Fitaccen Ɗan Wasa na Gasar, da kuma Ƙungiyar da Ta Fi Nuna Wasan Gaskiya, duk tare da kofuna.

Mai ɗaukar nauyin gasar ya kuma bayyana cewa za a fara rangadin nuna kofin gasar a faɗin jihar daga Litinin, 2 ga Fabrairu, 2026, zuwa Jumma’a, 6 ga Fabrairu, 2026.

Rangadin zai zagaya dukkan masarautun gargajiya 15 na jihar, farawa daga Masarautun Nafada da Funakaye, sannan ya wuce Yamaltu, Deba, Waja, Kaltungo, Tangale, Akko, Pindiga, Cham, Dadiya, Tula, Gona, da Dukku.

Ana shirya gasar Kofin Sarkin Gombe ta 2026 ne tare da ɗaukar nauyinta daga kamfanin Green White Green Sports Center Limited, tare da goyon bayan Mai Martaba Sarkin Gombe.

Ana sa ran gasar za ta ƙara bunƙasa harkokin ƙwallon ƙafa a matakin tushe tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin al’ummomin jihar Gombe.

Kwamitin shirya gasar na ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe a matsayin Shugaba, yayin da Auwal Musa Umar, tsohon Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta jihar Gombe, ke matsayin Mataimakin Shugaba.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya da wakilan al’umma, yayin da Haruna Abdullahi yake a matsayin Sakatare da Yakubu Maikudi Jami’an yada labarai tare da masu kula da harkokin yaɗa labarai da tallafin tsare-tsare na Musamman.

Labarai, Najeriya, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga
Next Post: Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
  • Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.