Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
Published: August 12, 2026 at 3:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta sun ceto mutane 23 da aka yi garkuwa da su, tare da hallaka ’yan ta’adda 19 a wasu samame da sintiri da aka gudanar a sassan kasar cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

A Zamfara, dakarun Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutane 18 da aka yi garkuwa da su a Sabon Gari, karamar hukumar Kaura Namoda, bayan da suka mayar da martani ga kiran neman agaji, lamarin da ya tilasta wa ’yan ta’addan tserewa.

A Jihar Filato kuma, sojoji sun ceto wani mutum da aka sace daga Duguri a Bauchi, yayin da Operation ENDURING PEACE ta hallaka wani dan ta’adda tare da kwato AK-47 da harsasai biyu.

A Kebbi, dakarun Operation FANSAN YAMMA sun hallaka ’yan ta’adda 18 yayin da suka kai hari kan jami’an Mobile Police Special Intervention Squad a Makuku, karamar hukumar Sakaba. Sojojin sun kuma lalata babura biyar tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu da aka kera a gida a wani samame a Filato.

A Borno, dakarun Operation HADIN KAI sun ceto mutane biyar da suka tsere daga wani sansanin ’yan ta’adda a yankin tsaunukan Mandara, bayan rikici ya barke tsakanin ’yan ta’addan. A Enugu kuwa, sojoji sun kwato AK-47 guda hudu, magazin bakwai da harsasan 7.62mm guda 133 daga maboyar masu garkuwa da mutane a dajin Umuchingu Ujenike.

A Taraba, dakarun sun kama mutane 19 da ake zargi da aikata laifuka a karamar hukumar Gashaka, tare da kwato babura, injinan famfo, wayoyin hannu da kudade. Rundunar ta ce ayyukan na daga cikin kokarin da take yi na amfani da bayanan sirri, sintiri da samame domin dakile ayyukan ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a sassan Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
Next Post: CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar Labarai
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.