Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu
Published: December 25, 2025 at 2:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 25, 2025

Gwamna Inuwa Yahaya Ya Taya Kiristoci Murna; Ya Buƙaci Su Ci Gaba Da Addu’o’in Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Jihar Gombe Da Najeriya.

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Kirista na jihar Gombe dama duniya baki ɗaya murnar bikin Kirsimeti na bana, inda ya bayyana bikin a matsayin lokacin dake karfafa ɗabi’un kauna, zaman lafiya, sadaukarwa da kuma haƙuri.

A saƙonsa na barka da Kirsimeti, Gwamnan yace bikin haihuwar Yesu Almasihu yana nuna muhimmin lokaci na yin nazari kan kyawawan halaye dake haɗa kan ƴan adam, ba tare da la’akari da addini ko asalinsu ba, sannan ya yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da ririta zaman lafiyan da suke yi da juna tare.

Gwamna Inuwa Yahaya yace jihar Gombe ta kasance misali mai kyau na jituwa tsakanin addinai daban-daban, inda mutane masu bambancin addini da ƙabilu ke zaune tare kuma suna aiki tare cikin girmamawa da fahimtar juna.

“Wannan lokacin biki yana tunatar da mu ikon ƙauna, tausayi da sadaukarwa waɗanda kyawawan halaye ne da ke da mahimmanci ga koyarwar Yesu Almasihu.”

“Waɗannan ɗabi’u suna da matuƙar muhimmanci wajen wanzar da zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna a jiharmu da kuma ƙasa baki ɗaya,” in ji Gwamnan.

Gwamna Inuwa Yahaya, wanda kuma shine Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa, ya yi ƙira ga Kiristoci su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan wajen yin addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai, kwanciyar hankali da wadata a faɗin jihar da Najeriya, musamman a wannan lokacin da ake buƙatar juriya da haɗin kai don shawo kan ƙalubalen tattalin arziki, tsaro da zamantakewa.

Ya kuma yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da jajircewa wajen tallafawa kokarin gwamnati na inganta walwalar jama’a.

Gwamnan ya tabbatarwa al’ummar Kiristan jajircewar gwamnatinsa na yancin yin addini, tabbatar da daidaito da kuma haɗa kan jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa zata ci gaba da damawa da duk al’ummar jihar a harkokin ci gaban da ake samu a jihar Gombe.

Ya kuma bayyana al’adar gwamnatin na bada tallafi ga kungiyoyin addini a lokutan bukukuwa don rage musu ɗawainiya, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin haɓaka haɗin kai da farin ciki tare.

Ya yi wa Kiristocin jihar Gombe da kewaye fatan alheri, farin ciki da cikar buri a bikin na Kirsimeti, yayin da ya yi ƙira ga duk ‘yan Najeriya su ƙara sadaukar da kansu ga haɗin kai, ‘yan’uwantaka da kuma zaman lafiya don ci gaban jihar da ƙasa baki ɗaya.

Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC
Next Post: Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
  • An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
  • Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.