Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu
Published: December 25, 2025 at 2:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 25, 2025

Gwamna Inuwa Yahaya Ya Taya Kiristoci Murna; Ya Buƙaci Su Ci Gaba Da Addu’o’in Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Jihar Gombe Da Najeriya.

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Kirista na jihar Gombe dama duniya baki ɗaya murnar bikin Kirsimeti na bana, inda ya bayyana bikin a matsayin lokacin dake karfafa ɗabi’un kauna, zaman lafiya, sadaukarwa da kuma haƙuri.

A saƙonsa na barka da Kirsimeti, Gwamnan yace bikin haihuwar Yesu Almasihu yana nuna muhimmin lokaci na yin nazari kan kyawawan halaye dake haɗa kan ƴan adam, ba tare da la’akari da addini ko asalinsu ba, sannan ya yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da ririta zaman lafiyan da suke yi da juna tare.

Gwamna Inuwa Yahaya yace jihar Gombe ta kasance misali mai kyau na jituwa tsakanin addinai daban-daban, inda mutane masu bambancin addini da ƙabilu ke zaune tare kuma suna aiki tare cikin girmamawa da fahimtar juna.

“Wannan lokacin biki yana tunatar da mu ikon ƙauna, tausayi da sadaukarwa waɗanda kyawawan halaye ne da ke da mahimmanci ga koyarwar Yesu Almasihu.”

“Waɗannan ɗabi’u suna da matuƙar muhimmanci wajen wanzar da zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna a jiharmu da kuma ƙasa baki ɗaya,” in ji Gwamnan.

Gwamna Inuwa Yahaya, wanda kuma shine Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa, ya yi ƙira ga Kiristoci su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan wajen yin addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai, kwanciyar hankali da wadata a faɗin jihar da Najeriya, musamman a wannan lokacin da ake buƙatar juriya da haɗin kai don shawo kan ƙalubalen tattalin arziki, tsaro da zamantakewa.

Ya kuma yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da jajircewa wajen tallafawa kokarin gwamnati na inganta walwalar jama’a.

Gwamnan ya tabbatarwa al’ummar Kiristan jajircewar gwamnatinsa na yancin yin addini, tabbatar da daidaito da kuma haɗa kan jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa zata ci gaba da damawa da duk al’ummar jihar a harkokin ci gaban da ake samu a jihar Gombe.

Ya kuma bayyana al’adar gwamnatin na bada tallafi ga kungiyoyin addini a lokutan bukukuwa don rage musu ɗawainiya, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin haɓaka haɗin kai da farin ciki tare.

Ya yi wa Kiristocin jihar Gombe da kewaye fatan alheri, farin ciki da cikar buri a bikin na Kirsimeti, yayin da ya yi ƙira ga duk ‘yan Najeriya su ƙara sadaukar da kansu ga haɗin kai, ‘yan’uwantaka da kuma zaman lafiya don ci gaban jihar da ƙasa baki ɗaya.

Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC
Next Post: Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.