Gwamnatin Jihar Neja Najeriya ta karbi sauran yara 130 da aka samu nasarar akarbowa bayan da wasu yanbindiga suka yi garkuwa dasu daga makarantar St. Mary dake garin Papiri a yankin karamar Hukumar Agwara.
Duk da yake dai kamar abaya babu wani karin haske akan yadda aka karbo wadan nan yara da aka sace, tun a farkon watan Nuwamban da tagabata, amma Gwamnan Jihar Umar Muhammad Bago yace yana cikin farin ciki akan samun yaran cikin koshin lafiya.

Dan Majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar yankin na Agwara da Bargu Hon. Jafaru Agwara, wanda shima ya taba tsallake rijiya da baya daga hannun yanfashin dajin. Yace duk da yake yankin na Agwara ya shiga yanayi na rudani amma yanzu sun fara samun kwanciyar hankali.

Shugaban karamar hukumar ta Agwara Iliyasu Zakari amadadin iyayen yaran, yace idan aka kalli yaran tabbas akwai ‘yar matsala shi yasa a yanzu haka an shirya jami’an kiwon lafiya da zasu duba su.

Har yanzu dai akwai wasu mata 14 na garin Ibeto, tare da wasu Mazaje biyar ciki harda Kwamishina a hukumar zaben Jihar Nejan Barista Muhammad Borgu na hannun yanbindigar a Jihar Nejan, da ake tsare dasu tun a cikin watan oktoba da ta gabata inda rahotanni suka tabbatar da cewa daya daga cikin matan ta mutu a cikin makon da yagabata.


