Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda
Published: December 23, 2025 at 2:18 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 23, 2025

Gwamnatin Jihar Neja  Najeriya ta karbi sauran yara 130 da aka samu nasarar akarbowa bayan da wasu yanbindiga suka yi garkuwa dasu daga makarantar St. Mary dake garin Papiri a yankin karamar Hukumar Agwara.

Duk da yake dai kamar abaya babu wani karin haske akan yadda aka karbo wadan nan yara da aka sace, tun a farkon watan Nuwamban da tagabata, amma Gwamnan Jihar Umar Muhammad Bago yace yana cikin farin ciki akan samun yaran cikin koshin lafiya.

Dan Majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar yankin na Agwara da Bargu Hon. Jafaru Agwara, wanda shima ya taba tsallake rijiya da baya daga hannun yanfashin dajin. Yace duk da yake yankin na Agwara ya shiga yanayi na rudani amma yanzu sun fara samun kwanciyar hankali.

Shugaban karamar hukumar ta Agwara Iliyasu Zakari amadadin iyayen yaran, yace idan aka kalli yaran tabbas akwai ‘yar matsala shi yasa a yanzu haka an shirya jami’an kiwon lafiya da zasu duba su.

Har yanzu dai akwai wasu mata 14 na garin Ibeto, tare da wasu Mazaje biyar ciki harda Kwamishina a hukumar zaben Jihar Nejan Barista Muhammad Borgu na hannun yanbindigar a Jihar Nejan, da ake tsare dasu tun a cikin watan oktoba da ta gabata inda rahotanni suka tabbatar da cewa daya daga cikin matan ta mutu a cikin makon da yagabata.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/PAPIRI-22-12-2025-1.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago
Next Post: Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.