Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Published: December 23, 2025 at 2:29 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 23, 2025

Wasu jami’an tsaron Najeriya sun bada tabbaci ga ‘yan kasar cewa babu wani abun tashin hankali ko fargaba gameda jiragen leken asiri na Amurka da suke shawagi a sararrin samaniyar kasar. Suka ce matakin ya faranta musu rai saboda Amurka tana taimakawa Najeriya ne ta fuskar tsaro.

Jami’an tsaron sun tabbatarwa Amurka Ke Magana cewa matakin na hadin gwiwa ne tsaknin jami’an tsaron Amurka da mayakan sama na Najeriya. Suka ce akwai sojojin sama na Najeriya a cikin jiragen da suke aikin leken asirin a sararin samaniyar kasar.

Jiragen suna tashi ne daga Ghana. Wannan matakin ya biyo bayan shawarwari da jami’an gwamnatin Najeriya suka yi da gwamnatin Amurka, bayan da shugaban Amurka Donald Trump, yayi barazanar kai hari kan Najeriya domin kare kiristocin kasar wadanda ake zargin ana yi musu kisn kare dangi. Gwamnatin Trump ta amince zata taimaki Najeriya ne bayan da aka gabatar mata da irin kalubale da kasar take fuskanta ta fuskar tsaro.

Gameda zargin gwamnatin Najeriya tana biyan kudin fansa kamin a saki mutane da ake garkuwa da su, musamman dalibai daga makarantu da ‘yan bindiga suke sace su, jami’an tsaron sun rantse da Allah cewa babu sisin kwabo daga aljihun Najeriya da yake fita domin biyan kudin fansa.

Daga nan suka yi kira ga ‘yan Najeriya su daina yi wa matakan gwamnati bahaguwar fahimta, maimakon haka a kullum su bukaci bayani, kamin su yanke shawara kan batu da  ya shafi gwamnati da al’uma.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya buga labarin zirga-zirgar jiragen leken asirin  sararin samaniyar Najeriya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda
Next Post: Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.