Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran
Published: March 25, 2026 at 3:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 25, 2026

Prime Ministan Pakistan Shebbaz Shariff, ya fada ranar talata cewa a shirye yake ya zama mai masaukin baki a shawarwari tsakanin Amurka da Iran na kawo karshen yakin na yankin Gulf, kwana daya bayan da shugaban Amurka Donald Trump, ya dakatar da barazanar da yayi na kai hari kan cibiyoyin wutan lantarki na Iran, cewa an gudanar da shawarwari masu ma’ana.

Duk da haka, Amurka tana shirin tura dubban karin sojoji daga runduna ta 82 zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda mutane biyu da suke da masaniya dangane da batun suka shaidawa kamfanin dillancn labarai na Reuters. Kari kan tulin dakarun da ta aike yankin, wadda hakan yake kara janyo fargabar yakin zai dauki lokaci mai tsawo.

A rubutu da ya wallafa a shafin dandalin sada zumunta na X, PM Sharif yace, Pakistan tana maraba, kuma tana bada cikakken goyon baya kan kokari da ake yi na yin shawarwari domin kawo karshen yakin.

Ahalinda ake ciki kuma, rahotanni suka ce Iran ta tsananta matsayinta kan shawarwarin yayinda tayi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila, kasuwar hannayen jari a Amurka ta fadi kasa, saboda fargabar babu alamar kakkautawa a rikicin da ake yi a yankin.

A wata kuri’ar neman jin ra’ayin jama’a da kamfanin dillancin labarai na Reuters da IPSOS, suka gudanar, ya nuna farin jinin shugaban Amurka Donald Trump ya zube zuwa kashi 36 cikin dari matsaya mafi karanci tunda ya koma fadar White House, saboda karin farashin mai.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta
Next Post: Isra’ila Zata Mamaye Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

https://www.youtube.com/watch?v=sainfSmn-EQ

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.