Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya
Published: January 12, 2026 at 8:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen China yace hukumomi a birnin Beijing su na jaddada goyon bayansu ga kasar Somaliya wajen karewa da tabbatar da ikon ta, da kuma dukkan yankunanta.

Wata sanarwar ma’aikatar harkokin wajen China ta ce Wang Yi, ya furta wannan a tattaunawar da yayi ta wayar tarho da takwaransa na Somaliya, a lokacin rangadin da yake yi a Afirka, inda ya kara da cewa China tana adawa da hada kan da yankin Somaliland mai neman ballewa daga Somaliya yake yi da hukumomi a Taiwan mai neman raba kanta daga China.

Tun da farko an shirya ministan harkokin wajen na China zai ziyarci Somaliya a bangaren rangadin sabuwar shekara da ya kai Afirka, wadda ta kunshi kasashen Habasha, Tanzaniya da Lesotho amma kuma daga baya an jinkirta ziyara zuwa Somaliya a saboda abinda ofishin jakadancin China ya bayyana a zaman sauya tsarin rangadin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku
Next Post: Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi

Karin Labarai Masu Alaka

Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
  • Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran Afrika
  • Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.