Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu
Published: January 2, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Gwamnatin jihar Gombe ta raba jimillar Naira miliyan 14 ga iyalan ’yan jarida bakwai da suka rasu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya faru a kan hanyar Billiri–Kumo.

Hatsarin ya auku ne a ranar Litinin, 29 ga Disamba, 2025, yayin da ’yan jaridan ke dawowa daga bikin auren wani abokin aikinsu da aka gudanar a Karamar Hukumar Kaltungo.

Kowane iyali daga cikin iyalan da abin ya shafa ya karɓi Naira miliyan 2 daga Gwamnatin Jihar Gombe a matsayin tallafin kuɗi domin taimakawa wajen ɗaukar nauyin jana’iza da sauran buƙatu masu muhimmanci.

Wannan tallafi na daga cikin ƙudurin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na rage raɗaɗin wannan babban rashi da ya faɗa wa iyalan da abin ya shafa.

Da yake jagorantar rabon tallafin a madadin Gwamnan, Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bayyana cewa tun farko an riga an bai wa iyalan waɗanda suka jikkata wani tallafi na gaggawa nan take bayan aukuwar lamarin.

Ya ƙara da cewa Gwamnan ya ɗauki dukkan nauyin jinya da kuɗaɗen asibiti na waɗanda suka samu raunuka kuma a halin yanzu suke karɓar kulawa a asibiti.

Farfesa Njodi ya jaddada ƙudurin gwamnatin yanzu wajen kula da walwalar ’yan jarida, tare da nuna alhini mai zurfi kan wannan babban rashi da ya shafi Jihar Gombe da kuma aikin jarida gaba ɗaya.

“Zuciyoyinmu sun kasance cikin baƙin ciki tun bayan wannan mummunan lamari, duk da cewa ba za mu iya dawo da waɗanda suka rasu ba ko mu biya diyya daidai da girman asarar, Mai Girma Gwamna ya amince da wannan tallafi domin taimakawa wajen jana’iza, tare da ɗaukar nauyin jinyar waɗanda suka tsira,” in ji shi.

Ya jaddada cewa kuɗaɗen ba diyya ba ne, illa alamar tausayi da jinƙai, domin tallafa wa iyalan a wannan mawuyacin lokaci.

Farfesa Njodi ya kuma isar da ta’aziyyar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ga iyalan mamatan, Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ), shugabanci da ma’aikatan Hukumar Talabijin ta Ƙasa (NTA Gombe), da kuma daukacin al’ummar kafafen yaɗa labarai, inda ya roƙi iyalan da abin ya shafa su karɓi lamarin a matsayin ƙaddarar Allah.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), Kwamared Alhassan Yahya Abdullahi, ya bayyana matuƙar godiya ga Gwamnatin jihar Gombe bisa abin da ya kira da tausayi da kuma tallafi na musamman da ba a taɓa ganin irinsa ba.

Ya ce ’yan Kungiyar NUJ a faɗin ƙasar nan suna matuƙar jin daɗin tallafin da aka bai wa iyalan mamatan da kuma ’yan jaridan da ke karɓar jinya a halin yanzu.

Kwamared Alhassan Yahaya ya kuma yi kira gwamnatin tarayya da ta hanzarta aiwatar da tsarin inshorar rayuwa da lafiya ga ’yan jarida, tare da roƙon gwamnatocin jihohi, ciki har da Gombe, su shiga cikin shirin da zarar an fara aiwatar da shi.

Babban Manajan NTA Gombe, Abubakar Adamu, ya bayyana godiyar Daraktan-Janar na NTA, Salihu Dembos, ga Gwamna Inuwa Yahaya bisa karamci da tausayi da ya nuna, inda ya ce daukacin iyalan NTA a faɗin ƙasar nan na girmama Gwamnatin jihar Gombe ƙwarai da gaske bisa wannan gagarumin tallafi.

Da yake magana a madadin iyalan mamatan, Barrista Abubakar Ahmed, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya kan wannan tallafi, yana mai bayyana shi a matsayin na farko irinsa a tarihin jihar Gombe.

“Wannan tallafi na Naira miliyan 2 ga kowane iyali zai taimaka matuƙa wajen biyan buƙatun gaggawa da na dogon lokaci na iyalan da aka bari, sannan haƙiƙa mun rasa kalmomin godiya, Allah Ya saka wa Gwamna da gwamnatinsa da alheri mai yawa,” in ji shi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya
Next Post: Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.