Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas
Published: March 19, 2026 at 3:41 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 19, 2026

Babban hafsan tsaron Najeriya, Olufemi Oluyede, ya bukaci al’ummomin jihohin Borno da Yobe da su kasance dasu ake yaƙi da ta’addanci, yana mai cewa hadin kai da goyon bayan jama’a na da matukar muhimmanci wajen kawo karshen rikicin.

Oluyede ya bayyana haka ne bayan tantance ayyukan rundunar sojin Najeriya kan yaki da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP.

Ya ce binciken ya nuna cewa nasarar ayyukan soja na da alaka kai tsaye da irin hadin kan da ake samu daga al’ummomin yankin. Ya kuma yi gargadin cewa ta’addanci ba zai yi karfi ba sai da taimakon wasu daga cikin jama’a.

A cewarsa, wasu rahotanni sun nuna cewa akwai mutanen da ke taimakawa ko boye ‘yan ta’adda, abin da ke kawo cikas ga kokarin sojoji tare da tsawaita wahalar da jama’a ke ciki.

Ya kara da cewa galibin masu aikata laifukan ba baki ba ne, illa mutanen da ake sani a cikin al’umma, ciki har da makwabta da ‘yan uwa.

Don haka, ya bukaci jama’a su daina jin tsoro ko nuna bangaranci, su rika tona asirin masu laifi tare da hana su mafaka.

Oluyede ya jaddada cewa yaki da ta’addanci ba aikin soja kadai ba ne, illa aiki ne na kowa da kowa, yana kira ga jama’a su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya kuma bayar da misali da wani hari a Kukawa, inda aka gano wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni suna cikin al’umma, abin da ke nuna yiwuwar hadin baki.

Babban hafsan ya tabbatar da cewa rundunar soji na ci gaba da kokarin dakile sabbin dabarun ‘yan ta’adda, ciki har da amfani da jirage marasa matuki (drones).

Haka zalika, ya bukaci sarakunan gargajiya, malamai, matasa da kungiyoyin farar hula su kara taka rawa wajen wayar da kan jama’a da yakar tsattsauran ra’ayi.

A karshe, ya bukaci ‘yan kasa su kasance cikin shiri, su rika kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba, tare da tabbatar da cewa rundunar soji za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin Arewa maso Gabas.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma
Next Post: Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.