Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas
Published: March 19, 2026 at 3:41 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 19, 2026

Babban hafsan tsaron Najeriya, Olufemi Oluyede, ya bukaci al’ummomin jihohin Borno da Yobe da su kasance dasu ake yaƙi da ta’addanci, yana mai cewa hadin kai da goyon bayan jama’a na da matukar muhimmanci wajen kawo karshen rikicin.

Oluyede ya bayyana haka ne bayan tantance ayyukan rundunar sojin Najeriya kan yaki da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP.

Ya ce binciken ya nuna cewa nasarar ayyukan soja na da alaka kai tsaye da irin hadin kan da ake samu daga al’ummomin yankin. Ya kuma yi gargadin cewa ta’addanci ba zai yi karfi ba sai da taimakon wasu daga cikin jama’a.

A cewarsa, wasu rahotanni sun nuna cewa akwai mutanen da ke taimakawa ko boye ‘yan ta’adda, abin da ke kawo cikas ga kokarin sojoji tare da tsawaita wahalar da jama’a ke ciki.

Ya kara da cewa galibin masu aikata laifukan ba baki ba ne, illa mutanen da ake sani a cikin al’umma, ciki har da makwabta da ‘yan uwa.

Don haka, ya bukaci jama’a su daina jin tsoro ko nuna bangaranci, su rika tona asirin masu laifi tare da hana su mafaka.

Oluyede ya jaddada cewa yaki da ta’addanci ba aikin soja kadai ba ne, illa aiki ne na kowa da kowa, yana kira ga jama’a su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya kuma bayar da misali da wani hari a Kukawa, inda aka gano wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni suna cikin al’umma, abin da ke nuna yiwuwar hadin baki.

Babban hafsan ya tabbatar da cewa rundunar soji na ci gaba da kokarin dakile sabbin dabarun ‘yan ta’adda, ciki har da amfani da jirage marasa matuki (drones).

Haka zalika, ya bukaci sarakunan gargajiya, malamai, matasa da kungiyoyin farar hula su kara taka rawa wajen wayar da kan jama’a da yakar tsattsauran ra’ayi.

A karshe, ya bukaci ‘yan kasa su kasance cikin shiri, su rika kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba, tare da tabbatar da cewa rundunar soji za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin Arewa maso Gabas.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma
Next Post: Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.